13: 1996

127 45 13
                                    


Nan da nan labari ya isa gidan biki cewar yaron Yaburra ya rasu. Nan yan biki suka dinga qarasawa gidan dan yiwa Yaburra ta'aziyya. Ba a bar gawar ya kwana ba nan da nan aka yiwa Hamza sutura aka kai shi makwancin sa Yaburra sai kuka tana kaicon ta ana ta kokarin rarrashin ta.

Gefen su Ibrahim suma gidansu taro suka yi na azo a gani duk da Hajia Falmata tace baza suyi wani babban taro ba sai amaryar su ta sama sauki tukunna. Da yamma yan uwa na jiki suka tafi asibiti suka duba Hadiza suka samu an bata magani tana ta barci. A nan suka sama labarin abunda ya faru da Yaburra suka ce aikuwa zasu qarasa gidan dan yi mata ta'aziyya.

Wani irin kallon takaici Daada tayiwa gashin Hadiza sabida irin askin kaskancin da Yaburra ta mata. Reza sabuwa ta samu ta kwashe ragowa gashin tas dan wani sabo ya taso. Yan uwan Maryama sun sha baqin ciki iri iri, sun sama kan su da yin dana sanin barin yaran a karkashin kulawar Haji Modu. Su kuwa Baba Azumi idanun su sun qara budewa, abunda ya faru ya ankarar da su cewar dole a tashi da yiwa Haji Modu addu'a dan ya rabu da asirin da ke tasiri a kan sa.

Mutane sun cika a gida Shatu ta fara ihu tana fadin "Maman mu ce ta cuce mu. Maman mu ce ta yi silar mutuwar Hamza". Tana kuka tana ihu kamar wadda ta zauce mutane suna riqo ta. Yan uwan Yaburra ne suka samu suka jawo ta aka rufe ta a cikin daki. Ita dai Yaburra tana gefe tana zubo da hawaye silently, wani sabon wutar tsanar su Hadiza da Fusam na ruruwa a zuciyar ta dan sune silar rashin Hamzan ta. Da ba dan su ba da Hamzan ta yau yana tare da ita. Alwashi ta dauka na raba su da duk wata farin ciki a cikin rayuwar su. Zata cigaba da azabtar da Fusam tunda Hadiza yanzu ta bar gidan amma itama zata san yadda zata yi da ita ta koya mata hankali.

A yammacin ranar Ibrahin ya wuce asibiti. Be tafi tare da kowa ba, shi daya yaje asibiti dan asalin sa ba wasu abokai gare sa ba, yan uwansa sune abokansa sai kuma abokan karatun sa wanda suke can qasar Canada. Yan kadan inda yike da su kuwa ba a wannan halin yike so su ga amaryar sa ba dan haka shi daya yayi tafiyar sa ganin ta. Koh da yaje har zuwa wannan lokacin tana barci.

"Yau barci take ta yi" Daada ta masa bayani "Jikin ya matsa mata jiya shine suka bata magunguna da allurai toh ina ganin su suka sa ta barci". Ta fada masa kan suka gaisa ta nuna masa farin cikinta tana masa Allah ya sanya alkhairi. Yan nasihohi ta shiga masa kan daga baya ta masa godia wannan babban taimakon da ya musu ya auri Hadiza zai dauke ta daga hell inda take da kuma kokarin da ya ce zai yi dan karbo Fusam sabida sun san koh sunce su zasu anshe ta Haji Modu bazai taba bari ba, amma dai kan su tafi zasu gwada luck din su su gani. Sai da suka gama magana tukun ta tashi ta futa daga dakin dan ta bashi privacy.

Kujerar da ta miqe daga kai yaje ya zauna, kusa da Hadiza. Karo na farko kenan a rayuwa da Ibrahim ya riqe hannun Hadiza cikin nashi. Ya jima yana kallon dan qaramin hannunta cikin nasa da ya fi girma. It looked perfect, like it was meant to be there all their life. Murmushi yayi kan ya kalli fuskar ta, looking peaceful in her sleep. Ya san ba jin sa zatayi ba amma hakan be hanasa yin magana ba.

"An daura auran mu Hadiza. Kin zama matata". Hakan ya kuma sa shi murmushi a zuciyar sa yana jin wani sabon so yana ratsa dukannin gabobin jikinsa. Kumatun ta ya shafa kan ya sake riqo hannunta ya zauna shuru, a million thoughts going through his mind, all happy thoughts about him and Hadiza, about the life they'll start together in ta warke, about the love and memories they'll share, the family they'll start. Tunanin ba qaramin annushuwa ya saka Ibrahim ba dan sai murmushi kawai yike ta saki. Da ka gansa ranar ka san yana cikin walwala.

Ya kai minti talatin zaune da ita bata farka ba har ya miqe ya futa daga dakin ya sama Daada zaune a waje ya mata sallama yace zai koma gida. Ga abinci nan ya kawo tayi kokari ta ci. Godia ta masa ta sa masa albarka kan ya wuce ita kuma ta koma cikin dakin. Hadiza bata farka ba ranar sai tsakar dare, nan da nan Daada ta hada tea ta dinga bata har ta sha ya ishe ta ta koma ta kwanta tana ta murmushi ita daya. Mafarkin Ibrahim tayi barcin da take barci, shi ke sa ta murmushi gashi kuma auran su da aka daura ranar. In ta tuna yanzu ta zama matar shi sai taji wani sanyi a ran ta, musamman yadda Daada ke qara yabon Ibrahim din tana fadin irin sa'ar da Hadiza tayi da samun sa. Nasiha ta fara mata akan Allah ta riqe shi amana da zuciyar ta tsakakkiya, tsakanin ta da Allah kada ta taba yin abunda zai cutar da shi dan shi din masoyin ta ne na asali.

Lawh-Al-MahfouzWhere stories live. Discover now