AƘIDA TA.

1K 42 5
                                    

_*AƘIDA TA*_

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Special thanks to all members of my Association
Perfect writers Association may Allah subhanahu wata'ala bless our pens and grant us wisdom to write what will bring positive changes to our Community.

I won't forget you my fans 😍😍😍 you are always in my heart, my love to you is endless, especially those that shows me love support and follow me with prayers since my first Novel to date, i can't mentioned you all but am proud of you all 😍

HAUSAWA SUKACE KYAN ALƘAWARI CIKAWA, KAMAR YADDA YAKE KOYAR WAR ADDININ MU CIKA ALƘAWARI ABU NE ME MATUƘAR MAHIMMANCI, NAZO DOMIN CIKA MUKU ALƘAWARI, A BAYA NASAKA RAN KAMMALAWA DA MAKARANTA A AUGUST, KATSAM AKA ƊAGA JARRABAWA AKA MAIDA ITA 20 GA WATAN SATUMBA, AMMA TUNDA NI NAYI MUKU ALƘAWARIN CIGABA DA KAWO MUKU WANNAN LITTAFI A WANNAN WATA, NA SHIRYA TSAF DAN CIKA ALƘAWARIN KU 'YAN AMANA, WATTANI HUƊU KUNA SAURARE NA, INSHA ALLAH BAZAN BAKU KUNYA BA, KU SHIRYA DOMIN SALON NA DABAN NE, AKWAI TUFKA DA WARWARARA ME MATUƘAR SARƘAƘIYA A WANNAN LITTAFI DA KUKA DAƊE KUNA JIRA.
KARA ƊAYA ZAKUYI MIN, SHINE NUNAMIN JIN DAƊIN KU TA HANYAR YIMIN COMMENT TARE DA SHARE, LITTAFIN NAN KYAUTA NE DOMIN JIN DAƊIN KU MASOYA NA, AMMA A DALILIN RASHIN COMMENT ƊINKU KOMAI NA IYA CANZAWA, GA MASU MANHAJAR WATPAD KU GARZAYA KU NEMENI
@AYSHERCOOL7724
KU NEMI LITTAFIN A FACEBOOK A
GROUP ƊIN PERFECT WRITERS ASSOCIATION
ƘOFA TA A BUƊE TAKE DOMIN GYARA SHARHI KOKUMA SHAWARA
AYSHERCOOL
07063065680

YADDA NA FARA LAFIYA ALLAH YASA IN KAMMALA LAFIYA

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

BISMILLAHIRAHMANIRRAHIM

ELEGANT ONLINE WRITER'S

*PART1*
_Page 4_

Babu alamar sassauci fuskar Widad, yanayin fuskarta ze tabattar maka da gaske har cikin zuciyar ta zata aikata abunda ta faɗa, ta juya ta koma cikin gidan da hanzari.

Jinjina kai Isa ya dinga yi yana kuma sake shafa kumatunsa yadda yske masa raɗaɗi, tare da tausayawa wulaƙancin da Yusuf ze fuskanta.

Ramla kam cikin sassarfa ta nufi ɗakin mahaifiyar ta, tun daga waje take kiran "Mummy"

Hajiya Halima tace "Ramla wannan wane irin kira ne haka? Ke kam bakya girma"

Ramla ta ƙarasa kusa da mahaifiyar ta ta zauna tace "wai nikam nace me akayiwa 'yar gwal ne? Naga kaman ciwon nata na ƙoƙarin tashi fa? Kuma ga dukkanin alamu yau ta kwaɓe mata itada uban tane"

Ɗan tsaki Mummy tayi tace
"sakani yake cikin sha' aninsa shida 'yar sa ne? Ai sedai inga suna lamauran su ta yaya zan san meya sameta?"

Ramla ta sake gyara zama "hmm kinsan dai halin ciwon ta, a corridor ɗin ƙasa na haɗu da ita, tana ta surutai, wai Daddy Aure zeyi mata, se safa da marwa take tana zufa"

Zaro ido Mummy tayi tace "Aure kuma? Wane irin Aure ana zaman lafiya? Waye ze Auri mahaukaciya mara tarbiyya kamar wannan Yarinyar? Shi mijin da haukan zeji ko kuma da rashin tarbiyya?"

Ramla tace "waya sani musu?, sedai ki jiyo mana kanun Labaran muma ki fesa mana, Amma ina tunanin wanda ze kwashi wannan Mahaukaciyar"

"To nidai a iya sanina bata yadda da mutane ma, to ta yaya ta samo wanda ze Aure ta?"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now