AƘIDATA CHAPTER 30_31

560 43 0
                                    

                    _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 30_31

Yusuf ya tsaya cak ya waigo ya kalle ta yace "are you serious kin amince?"

Shiru tayi, taƙi ce masa komai, har yanzu izzar tana nan, abune mawuyaci ta maimaita magana sau biyu, Yusuf yace "Shikenan, idan Saleh yazo zanyi masa magana, kokuma in samu maigari in masa bayanin komai"

Gyara kwanciyarta tayi tace "kuma ranar da zamu koma gida zaka sakeni,gara kasa wannan a ranka"

Yusuf yayi murmushi yace "karki damu, nidai fatana ki samu lafiya komai ya lafa mu koma gida"

Nurat ta koma gida, ta lallaɓa zata silale ta shiga ɓangarenta, "daga ina kike?"

Taji muryar mahaifinta, tsayawa tayi amma takasa cewa komai, cikin tsawa yace "Nace gidan ubanwa kikaje?"

"Amm.. Ammmm. Dama... Damanaje gidansu ƙawata ne shine....

" shine ubanki, yaushe kika fara fita ke kaɗai babu direba? Daga gidan ubanwa kike? Zaki gayamin ko sena kwantar dake na yankaki a gurin nan"

Nurat ta faɗa a Shagwaɓe "Nifa ba inda naje"

"Ubanwa ya kaiki duba Daula a Asibiti ubanki ne?"

A razane ta ɗago ta kalleshi, ta shiga rarraba ido.

"ba magana nake miki ba?"

"Daddy waye ya gaya maka naje duba shi?"

"Ubanki ne ya gayamin" Alhaji Musa ya bata amsa

"Kin san a duniya mutumin nan maƙiyinane, shine kika kwashi jiki kika tafi?"

Nurat tace "Daddy, 'yarsa ƙawatace kuma dukda abunda ke tsakaninku tazo gidan nan birthday na ta bani kyautar mota, yanzu kuma a sace ta mahaifinta a gadon Asibiti in kasa duba shi"

Kafin ta ƙarasa ya ɗauketa da mari, wanda seda ta dena gani na wani ɗan lokaci.

Da sauri Mahaifiyar Nurat ta fito tana cewa "lafiya kuwa? Me tayi maka ne?"

"dole ki tambayi me tayimin mana, munafuka daga ke har ita, wato da saninki ta fita taje Asibiti duba Daula, babban maƙiyina ko?"

Mahaifiyar Nurat tace "haba Alhaji kai waye ya gaya maka can taje"

Alhaji musa yace "Rufemin baki kafin in haɗa dake in muku duka, na wuce duk yadda kuke tunani, duk wani motsinku a waje ina da masu kawomin rahoto, kuma daga yau na saka doka, kada ki kuskura Nuratu ta sake fita daga cikin gidan nan, ban yadda ta sake zuwa ko'ina ba, idan kuwa ta sake sena saɓa muku daga ke har ita"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now