AƘIDATA CHAPTER 40_41

631 39 3
                                    

_*AƘIDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED

ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 40_41

Gaban Nurat ne ya shiga bugawa da sauri da sauri, ta shiga zazzare ido be kula ta ba bece mata komai ba, tazo ta tsaya tana kallon sa, taga harta wuce bece mata uffan ba.

Ta shiga ɗaki ta nemi guri ta zauna, tayi shiru tana tunanin yadda zata samu Anwar ya kuɓuta, babu zato taji an murɗa ƙofar ɗakin nata.

Mahaifinta ne ya shigo yana rarraba ido, gadan gadan yayo kanta yana faɗin "gidan ubanwa kika je?"

Miƙewa tayi a gigice ta shiga ja da baya tana faɗin "babu inda naje Daddy"

"ƙarya kike munafuka, harni zan saka doka ki sa ƙafa kiyi fatali da ita? Uwarki ta ɗaure miki gindin kiyi rashin mutunci ko? Ni da Daula waye ya haifeki?"

"Daddy niba gurinsa na je ba, Ai an ɗauke shi daga Asibiti"

Sekuma yayi sak, "Ubanwa waye ya gaya miki?"

"wallahi Daddy a gari naji"

"to gidan ubanwa kikaje? Zaki gayamin ko sena yanka ki a gidan nan?"

Girgiza kai take, takasa magana ya cakumo wuyanta yana zazzare ido, kakari ta dinga yi tana kuka tace "Wallahi Daddy ba inda naje, kawai gajiya nayi da zaman gidan na fita, dan Allah kayi haƙuri"

"se naci ubanki yadda idan na sake saka doka ba zaki takamin ba"

Cikin kuka Nurat tace "Wayyo Allah Mummy, ki temakeni karya kasheni"

Maimakon ya saketa sake shaƙeta yayi, yana kuma zaro mata ido kamar tsohon maye.

Kakarin Nurat ne yasa mahaifiyar ta, ta sallame salar da take, a guje ta rugo ɗakin Nurat, ta tarar ya shaƙe Nurat kamar ya kama sa'ansa ko kuma wani shahararren Ɓarawo.

"Kayi haukane, ka cikamin 'yata ita kaɗai ce dani, kana gani duk yaranmu mutuwa suke, ita kaɗai Allah ya barmin ka ƙyalemin' yata"

Juyowa yayi a fusace ya mangare mahaifiyar Nurat yace "itama ɗin gara in aikata inda waɗancn suka tafi, muddin zata dinga takemin doka, tasan a duniya bani da maƙiyi sama da Daula, danme zata dinga zuwa inda yake, akan me?"

Yai maganar tare da wurgi da Nurat, wadda tuni ta fara fita a hayyacinta, dan daya jefar da ita ko motsi ba tayi, se kokawa take da numfashi.

Da sauri Maman Nurat ta nufi kan Nurat, yayin da Alhaji Musa ya cigaba da banbami, ta ɗago Nurat sedai bata numfashi.

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now