AƘIDATA CHAPTER 11

592 36 3
                                    


_*AƘIDA TA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Special thanks to all members of my Association
Perfect writers Association may Allah subhanahu wata'ala bless our pens and grant us wisdom to write what will bring positive changes to our Community.

PART1
Page 11

Bin motar Yusuf yayi da kallo harta ƙure, sannan a sannu yaja ƙafar sa ya ci gaba da tafiya abubuwa daban daban na yawo a kwanyarsa.

Maimakon ya tafi gida seya tsaya yayi sallar azahar ya wuce gurin aiki, office ɗin Abbas ya tafi yaje ya tarar da shi yana tsaka da wani aiki, Abbas na ganin Yusuf yai murmushi suka gaisa sannan yace
"Yane mutmina? Akwai wani latest update ne?"

Yusuf ya ɗan ɓata rai yace "na baka abu kayi assisting ɗina kaƙi, seni nayi abuna bakomai nagode"

"wane abu kace inyi assisting ɗin naka naƙi?" Abbas ya tambaya

"Akan mahaifin yarinyar nan Nurat mana, Nace ka tayani bincike akansa amma ƙarshe ni nayi abina"

Dafe kai Abbas yayi yace "Sorry my man, wallahi aiki yayi min yawa na manta shaf"

"Shikenan amma ina tafe da Labari ne"

Abbas ya tattara hankalin sa yace "ina jinka, dama kamar kasan jiya Oga Suleiman yayi min maganarka"

Yusuf yace "Abbas ina kyautata zaton akwai sa hannun matar Mahaifin Widad a farmakin da'ake kai musu"

Abbas ya ture System ɗin gabanshi ya sake tattara hankalinsa yace "ta yaya kenan? Meka gano?"

Nan Yusuf ya gaya masa abubuwan da Su Hajiya Halima keyi, da kuma Yadda suka yi da Ramla"

Jinjina kai Abbas ya shiga yi yace "Lallai biri yayi kama da mutum, amma kaga Oga yana Abuja akan wani case, Amma idan hakane meye alaƙar iyalan Alhaji Nasir da Mahaifin Nurat?"

Yusuf yace "Abunda zan ɗora da bincike na akai kenan"

Waya ce ta fara ringing, Abbas da Yusuf suka shiga waige waigen wayar da take ringing ɗin, Abbas yace "kamar daga jikin ka ringing ɗin ke tashi fa"
Se yanzu Yusuf ya tuna an bashi sabuwar waya, hannu yasa ya ɗakko wayar ya ɗaga, suka gama magana Umma ce ta kira shi.
ssebayan Yusuf ya gama Abbas yace

"jar uba mutumina wannan latest phone ɗinfa? Miƙomin in ganta, yaushe ka siyi waya haka, kaida manyan wayoyi basu dame ka ba?"

Yusuf ya miƙa masa wayar yace "Widad ce ta aikeni na siyo mata wayoyi masu tsada guda biyu, ina kai mata ta bani wannan"

Abbas ya dinga jinjina kai yana jujjuya wayar yace "Lallai ka faso gari, amma kamata yayi ka siyar da ita kai sabgar gabanka da kuɗin"

"Idan kuma ta tambayeni wayar nace na siyar taji daɗin Yimin wulaƙanci ko?"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now