AƘIDATA CHAPTER 26_27

509 40 1
                                    

                    _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

(GAMAYYAR MARUBUTA NA ELEGANT ONLINE WRITER'S, INA GODIYA DA KARRAMANI DA'AKAYI DA CERTIFICATE NIDA ƘUNGIYATA TA PERFECT WRITERS ASSOCIATION, INA GODIYA DA WANNAN KARAMCI UBANGIJI ALLAH YA ƘARA HAƊA KAN MARUBUTAN MU AMEEN, INAWA KOWA DA KOWA FATAN ALKHAIRI, TARE DA FATAN KOWA YAJE GIDA LAIFIN)



ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 26_27

Gaba ɗaya Widad ko motsi ba tayi, Yusuf ya rungumeta sosai a jikinsa kamar wani ze ƙwace masa ita, zuciyar ta na bugawa amma numfashinta baya fita sosai, ga cikinta se ƙara yake saboda yunwa.


Anwar ya kai Nurat gida, suka yi Sallama, ta shige gida jikin ta na rawa ta tafi ɗakin mahaifiyar ta.

"ke ina kika fita kikaje ban sani ba?"

"Mummy akwai matsala fa"

Cike da rashin fahimta mahaifiyar ta tace "matsalar me?"

"Widad ta ɓata an sace ta"

Dafe ƙirji tayi tace "innalillahi wa inna ialaihi raji'un, waye ya gaya miki?"

"Mummy can naje fa, Daddynta yana Asibiti ma naje na duba shi ma"

Zaro ido tayi tace  "ubanwa yace kije? Sekin jawa kanki faɗa a gurin mahaifinki ko? Tashi maza kije ki cire hijjabin nan ki huta"

Nurat ta kalli mahaifiyar ta tace  "Mummy, Daddy ne fa yasa aka sace Widad"

"inji ubanwa? Rufen baki shashasha, in kika sake maganar nan yaji kema zeyi maganin ki"

"Mummy a matsayinki na uwa, ya zakiji idan ni aka sace, yakamata ki cire tsoro a ranki ki gayawa babana gaskiya, ranar da hakki ya tashi bashi kaɗai ze kama ba harmu"
Ta ƙare maganar tare da ficewa daga ɗakin gaba ɗaya

Kwata kwata duk bidirin da'ake Fahad beje yaga jikin Alhaji Nasir ba shima kuma Alhaji Nasir be tambaya ba, yana fama da kansa.

Mussaman Abbas daga inda yake aiki ya kira Umman Yusuf ya sanar da ita ɓatan ɗanta, dama ta kira wayar Yusuf harta gaji bata shiga.
Aikuwa ta kiɗime sosai ta tashi hankalin ta, ta shirya ta tafi gurin aikin Yusuf.

Ma'aikatan su kansu a kiɗime suke tun bayan da suka samu labarin ɓatan Yusuf, Suleman yayi duk yadda zeyi a basu damar bincike akam al'amarin amma daga sama aka hanasu, akace an riga an danƙa case ɗin a hannun wasu jam'ian tsaron.

Sosai Umman Yusuf tasa Abbas a gaba tana zabga kuka
"dan Allah ranka ya daɗe ina ɗana yake? Ku kuka sashi aikin nan ina kuka turamin shi shi kaɗai nake kallo inji daɗi, Yusuf ne kaɗai dani, dan Allah ku temaka ku nemomin Yusuf ɗina"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now