AƘIDATA CHAPTER 24_25

535 49 9
                                    

_*AƘIDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 24_25


Gaba ɗaya ma'aikatan gidan su kayo kan Alhaji Nasir, sedai jikinsa kamar babu rai, 'yan sanda suka ƙaraso cikin gidan aka kwashi Alhaji Nasir a daren zuwa Asibiti.

Widad kam gajiya tayi da zaman motar, saboda tafiya suke bata wasa ba cikin wani irin azababben gudu, jin tafiyar taƙi ƙarewa ne yasa Widad fara mustu mutsu, tun tana mutsu mutsun har bacci ya kwashe ta, a firgice ta farka ta kurma wani uban ihu tana kiran
"wayyo Allah na Yoseef, karka tafi ka barni"

Yusuf yace "Widad ina nan, muna tare har yanzu Allah ze fitarmu insha Allah, ki dena shouting karsu miki wani abun"

Me tuƙa motar yace gara dai kaja mata kunnen.

Memakon tayi shiru ta cigaba da ihu tana "ku ƙyalemu mu tafi, yoseef na gaji da zaman nan hannuna igiyar nan ta dameni, bayana ciwo na gaji bayana ze karye"

Wata hoda su watsawa Widad, wanda hakan yasa ta baccin dole, ba Widad ba har Yusuf gaba ɗaya bacci ya kwashe su.

Ana kai Alhaji Nasir Asibiti, aka kwantar da shi aka dinga masa allurai da ƙarin ruwa, ga oxygen ansa masa domin temakawa numfashinsa dake barazanar ɗaukewa.

Likitoci suka duƙufa akansa, suna bashi dukkanin taimakon da zasu iya, ga jininsa ya hau fiye da kima suna ta ƙoƙari jininsa ya sauka.

Yusuf ne ya fara farkawa jin motar ta tsaya, aka buɗe motar suka kwance musu ido, mamakine ya kama Yusuf, tun cikin dare suke tafiyar nan amma da'aka kwance musu ido yaga yanayin garin kamar Azahar ta gota, daji ne sosai ciyayi sun lulluɓe ko ina, gaba ɗaya Yusuf baya gane inane gabas ko yamma ya kasa gane ta ina suka zo nan gurin.

Widad kam sam bata hayyacinta, ta farka amma se tangaɗi take haka suka sasu a gaba zuwa wani gini.

Yusuf yayi mamakin yadda aka shigo cikin wannan uban dajin akayi ginin gida, suka buɗe gidan suka shiga dasu Yusuf.

Gaba ɗaya gurin kango ne, kuma ga dukkanin alamu an samar dashi ne mussman saboda wannan aikin, saboda gurin sabon gini ne harda ragowar kayan aikin ginin.

Wani ɗaki suka kai su Widad suka ajiye, akan tsurar tabarma suka kawo musu ruwan pure water guda biyu suka ajiye musu suka maida ƙofa suka rufesu a ciki.

Yusuf ya ɗau ruwa ɗaya ya fasa ya bawa Widad, aikuwa nan da na ta zuƙeshi da alama tana jin ƙishirwar sosai, ga ko salla ba suyi ba haka ya zuba mata ruwa tayi alwala, ɗan ragowar shima yayi ba tare da sun san inane gabas ba haka suka gabatar da salla.

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now