41

432 48 6
                                    


A hankula ya sake ta jin zuciyar sa tana raya masa abubuwa da dama, miƙewa ya yi yana faɗin bari inje nasan anata jirana a office sai na dawo anjima. Bari in je in faɗawa Hajiya tazo tayi godiya inji Ummu hanin.

Kinjiki dan Allah ki kyale ta ai ba wani abu bane.

Murmushi ta yi masa tom shikenan nawan Allah ya kiyaye hanya Amin ya ce yayin da Ummu hanin ta ce yawwa anjima zani in ma Salman albishir, ki ce kawai zaki yawo Malama Faruk ya bata amsa.

La'ila daman Salma ta faɗa bazaka dinga barina ina zuwa ganin su ba.

Murmushi ya yi ah kice zugaki take tom zan haɗu da ita ne.

A'a fa mijin Ummu hani kaima kasan dai ba zuga bace tunda yaushe rabon da in tambaye ka unguwa yau daga tambaya ka ce yawo.

A'a dai ko shekaram jiya kinje gidan Kawu, ya faɗa yana tsure ta da ido, dariya ta yi yo wannan ai fitar ka ce, kaine kasa naje in tani ne a shekara ba'a tare ba, kaine sarkin rashin haƙuri.

Ah lallai yarinyar nan, ai wallahi ki bari kawai bazaki gane banda hakuri ba sai..... Nidai inje dan Allah ta roƙa cikin sanyayyiyar murya, naji ki je anma karki jima kuma banda cin ado.

Riƙe haɓa ta yi tana kallon sa dariya yasa ni dai na faɗa miki banason ana gane min gayun ki.

Yo to banda abin mijin Ummu hani ai Ummun tasa ba wani haɗuwar da intayi gayu zataja hankali tayi ba.

Kai ah lallai ma ke kinsan yadda kike da jan hankali kuwa musanman in kina wanna takun, yaɗan gwada tafiyar ta, salati tasa cikin dariya shima dariyar yasa ya ce muje ki karɓi Admission letter ɗin ya yi waje yana dariya, itama tom ɗin kawai ta ce cikin dariyar gami da zarar mayafi ta fito tsakar gida ɗakin hajiya ta leƙa ta ce Hajiya zan amso takar da a motar Faruk.

Tom karki daɗe Hajiya ta ce.

Bayan Faruk da tuni yayi waje ummu hani tabi dan karɓo takardar, a cikin mota ta same shi ta ɗan matsa kusa dashi ya miƙo mata takardar ta amsa tana murmushi sai da ta karanta sannan ta hau godiya harar ta yayi kedai bakya gajiya da godiya ni bara in wuce.

Har ta juya ya ce kinga nama sha'afa wallahi, dawowa tayi da ido ya nuna mata ta shiga motar.

Zagayawa ta yi ta shiga dan tuni yaɗan zura hannu ya buɗe mata.

Shaf daɗin abincin ɗazu ya mantar dani shekaran jiya naje na miki registration na waec tunda a SS2 kika dena zuwa na kuma miki registration na lessons kafin ayi exam ɗin.

Kasama magana tayi sabida farin ciki, kamar yasan abinda ke ranta kenan sai dai tana ganin ya wuce tasa shi yayi abinda baida ra'ayi kodan iya halaccin sa na ɗaukan ƙannen ta tamkar nasa koma tamkar ƴaƴan sa.

Bakice komai ba niyata tunda exam din may june ce in kika tare agida sai masu lesson din su dinga zuwa suna koya miki da nace can sch din zaki dunga zuwa sai suka ce suna private service ma.

Kawai kallon sa take tana murmushi ta rasa mai zata ce ta ko ina Faruk rahamane a rayuwar ta ayanzu da take kuma kallon sa hasaso irin sa'ar datayi na samun sa a miji take.
Matsowar da yayi daf da ita ne yasata saurin kallon sa.

Belt yahau sa mata ta ce ah me kake haka, ɗaga mata gira yayi gami da sakar mata Murmushin da yasa tsigar jikin ta tashi tayi saurin kawar da kai.

Tafiya zan da ke, a tsorace ta matsa ina kuma.

Tun ɗazu nake magana kinƙi magana, kawai kallon ki da nake ɗan mintoci kina murmushi sai zuciya take faɗan sati shida yayi yawa wallahi.

Basar dashi tayi tahau godiya, ni kinga ba godiya zakimin ba, ai godiya ta zama dole Nagode Allah ubagiji ya saka da Alheri, rufe mata baki ya yi wai mene na godiya kefa matata ce nemar miki illimi dole nane, Ni dan Allah ki yadda mu tafi kawai gobe nazo in tafar miki da kayan ki.

Dariya tayi gami da ɗauke hannun sa abakin ta, kan ta ce yanzu dai goben da yaushe zamu gun registration ɗin da ka ce za'ai pinger print ɗin.

Kallon da yake mata yasa ta buɗe motar sai anjima ɗin in ka dawo zamuyi maganar.

Binta ya yi da kallo sai sa ta ɓacewa idanun sa sannan ya tuno da batun da sukayi da Abban sa shikam bai san ta yadda zaiyi ya faɗawa Ummu hani wai da kishiya zata tare ba, kuma wai Fatima shi bai san ta yadda zai iya faɗa mata cewar auren dole ne za'a masa ba.

Koda Ummu ta koma gida da gudu ta shige ɗakin Hajiya cikin murna take nuna mata Admission Letter ɗin murna Hajita tasa itama ta hau sawa Faruk albarka.

Sai da suka gama murnar Hajiya kewa Ummu hani faɗam me yasa bata Faɗa mata tun faruk yana nan ba ta yi masa gidiya.

Wallahi Hajiya na ce zanzo in faɗa miki kinsan Halin sa ya nuna wai ai ba komai bane, anma ai yace anjima zai dawo sai ki masa godiyar.

Tom shikenan Allah ya dawo dashi lafiya yayi masa albarka yasa ku anfani juna a zaman nan naku.

Amin Hajiya nima ya ce ya biyamin kuɗin exam yace zan cigaba da karatu.

Murnar Hajita ta yanzu har ta fi ta ɗazu dan tasan yadda Ummu hani ke som karatu kawai sabida ƙannen ta ita ta watsar da nata burin.

Nan tayi ta sawa Faruk albarka yayin da Ummu keta faman amsawa da amin.

Wurin huɗu Ummu hani tayi wankan ta tsaf ta yi kyau sosai ta ɗauki Muhammad sukayi gidan su Salma bayan ta faɗawa Hajiya zataje ta kaiwa Salma admission letter ɗin.

Akofar gida ta haɗu da Faruk mamaki ya cika ta badai har ka dawo ɗin ba.

Zuwa nayi ko ki tawo mu tafi ki tare yau ko ni in dawo gidan nan kawai.

Ɗan zaro ido ta yi tana kallon sa kan ta ce wani abu ya zagaya bayan mota ya fito da jaka this are my things it's either ki ɗauko kayanki ko ni in shigar da nawa ciki na dawo nan in sati shidan ta yi ma tafi tare sakato ta yi tana kallon sa ya ce oya am waiting what's your answer.....

Ummu HaniDonde viven las historias. Descúbrelo ahora