p.....8

421 34 0
                                    

🍅🍅🍅🍅🍅🍅🍅🍅🍅🍅🍅

    *🤦‍♀️🤦‍♀️KOMAI NUFIN ALLAH NE🤦‍♀️🤦‍♀️*

  *By*

*DEEJAH*
     *(UMMU FU'AD & AFNAN)*

*MARUBUCIYAR*
*1-RASHIN UWA*
*2-RAYUWAR GIDAN KAWONA*
*3-KALAR TAWA KADDARAR*
*4-RAYUWATACE HAKA*

AND NOW IS

*KOMAI NUFIN ALLAH NE*🤦‍♀️

🅿️0️⃣8️⃣

*Agaskiaya zan daina typing saboda Babu comment Kuma sai ayita yimin magana ana fadin sis kwana biyu ba'ayi Mana typing ba, sis please yau ayi typing book din akwai dadi, sis ataimaka Mana da ko read more dayane*😉😉😉😉😉😉😉 *to yaseen nagaji zan ajiye idai Babu comment banga amfanin yiba*

  Hajiya ce ta sauke nannauyar ajiyar zuciya tayi shiru Tama rasa abinda zatace,
  Jin shashshekar kukana yasa suka fahimci Ashe natashi Nan hajiya ta karaso bakin gadon da nake kwance ta zauna kusa Dani tare da taba jikina tace
   "Deenah sannu kintashi ya jikin"
Mikewa nayi zaune tare da fadin
  "Hajiya Ina kwana ya gida?"
  "Lafiya kalau Deenah y jikin naki?"
"Naji sauki"
Kallona tayi sannan tace
  "Kukan me kikeyi haka Kuma ko jikinne har yanzu"
Girgiza Kai nayi nace
"Ah,ah Babu komi"
Kallon Ammi tayi take
  "Ammin deenah bari naje gida zan Aiko deejah ta kawo Mata magani insah Allah idon tashi zataji dama dama"
Nan ta tashi suka fita da Ammi suna magana,
 
  Bayan Ammi ta rakata tadawone take cemin
"Allah sarki hajiya kinji me tace Wai zatayi Miki wasu addu'o'i da akeyi na karya sihiri"
   Murmushi nayi ce
"Angode Mata sosai Allah ya saka da Alkairi"
"Ameen Ameen ai hajiya akwai kirki sosai tace zatazo cikin satin Nan Wai zamuyi magana"
Kallonta nayi nace
"Maganar me?"

"Wallahi ban saniba sai tazodin maji nasandai bazai wuce akan maganar da mukayiba"
  Shiru nayi nakoma na kwanta a Kan kujerar dake dakin namu,

Sai wurin karfe uku sannan deejah tazo tasameni kwance don ciwon Kai nakeyi sosai banako son ganin haske a cikin idona,
Shigowa tayi cikin dakin tare dayin sallama tace
  "Sisi nah sannu ya jikin?"
Zaune natashi nace
"Dasauki ya makaranta?"
"Alhamdulillah mukarasa haddar yau gabaki daya keda Shahid ne kawai bakuzoba Kuma ance cikin satin Nan za'a tsaida Data din sauka, dakuma kudin"
Murmushi nayi nace
"Allah yasa xanyi don na lallaine nayiba kuwa" kallona tayi cikin mamaki tace
  "Allah ya kiyaye ace za'ayi saukarmu babuke wallahi da nima saidai nafasayi" takarasa fuska ahade,
Murmushi kawai nakeyi sannan tace
"Ina Ammina take?"
"Tana dakin Abba nasan gyaramai takeyi yanzu Zaki ganta, Ina yayana?"
"Yana wajen aiki yanzu mukayi waya Wai idon nazo zai Kara Kira kugaisa"

"Allah sarki yayana"
Ammi ce tashigo dakin tare da sallama,
  Amsawa mukayi ta karaso fuskarta dauke da fara'a tace
  "Ashe diyatace dama naga takalmi nace kila kece sannu da zuwa ya hajiya taje gida?"
  Cikin murmushi tace
"Lafiya kalau, Ammi Ina yini ya gida ya maijiki?"
"Lafiya kalau taji sauki gata nan"
Murmushi tayi tace
"Gashi inji Ammi tace yanzu Tasha guda biyu saikuma gobe "
Tafada tana mikawa Ammi sannan ta mikomin kulan hannunta tace
  "Gashi Nan kici wlh tace idon baki ciba na fada mata"
Hade fuska nayi nace
"Ai banice keba kinsani"
"Zakiyi bayani ai nasan halinki bakison cin abinci idon baki da lafiya hakama magani sai anyi da gaske kikesha"
Banza nayi da ita nafara niyyar bude kular da takawomin,
  Abincine aciki shinkafa da taliya sai nama sosai akai, kallon Ammi nayi da take kokarin shigewa cikin daki nace
"Ammina Kinga harda abinci hajiya ta aikomin dashi"
   "Allah sarki hajiya mun gode da kokarin da take agaremu Allah ya biyata da mafificin Alkairi, Allah yabar zumunci"
  "Ameen Ammina ai bamu da abinda zamu biyata dashi sai addu'a"
"Hakane wannan Allah yaji Kan magabata, saiki kokarta kici don nasan hali yanzu sai..."
Shagwabe fuska nayi tare da saurin tareta nace
"Ammina zanfaci kina ganin Yansa ido anata kallona" nafada Ina hararta ta gefan ido,
  Dariya tayi sannan tace
"Ammina barta ai nasan komai shiyasa nazauna sainaga yadda zataci don wallahi saina fadawa hajiya idon bataciba" shiru nayi nafara cin abincin,
  Sukuma sunata firarsu har Ammi tashige dakin sannan ta juyo wajena zata Fara magana sai wayanta yayi Kara,
   Kallona tayi take
"Yayane yake Kira
  Murmushi kawai nayi Ina cin abinci,
Saida ta daga wayan sukayi magana sannan ta juyo wajena tare da fadin "gatan Nan tanacin abinci na tsareta"
Shiru tayi sannan tayi dariya tare da mikomin wayan
  Sallama nayi tare da gaidashi ya amsa yace
"Kanwata ya jikin naki?"
"Dasauki yayana"
"Allah ya Kara sauki, kiyi hakuri da kalar rayuwar da Kika tsinci kanki aciki kinsan kowa da kalar nashi kaddarar ke kalar taki kenan kiyi hakuri Kuma kidage da addu'a akan duk abinda ke damunki, dakuma abinda yake Shirin shiga tsakaninki da mahaifinki kokuma nace yashiga tsakaninki dashi" murmushi nayi Wanda ake Kira da yafi kuka ciwo sannan nace
"Insha Allah zandage da addu'a Akan wadda nakeyi ngd sosai Allah yabar zumunci nagode"
"Babu komai ai anzama daya, ya mamanmu?"
"Lafiya kalau take"
"Masha Allah kigaidamin ita kafin mazo nagaidata da kaina"
"Zataji insha Allah ngd"
Nan mukayi sallama na mikawa deejah wayar wadda take rike da wayana tana kallon pic aciki,
  Saida suka danyi magana sannan sukayi sallama,

  Bayan ta ajiye wayan muka Fara fira inaci gaba dacin abincin,

************************

Tun lokacin daya Fara waya da deejah yashigo office dinsa yazauna har lokacin da tabawa Deenah Yana zaune sai bayan ya Gama wayar ya ajiyene ya kallenshi tare da dauke Kai yacigaba da abinda yakeyi,
  "Malam kana ganina nashigo office dinka zaka wani kaudakai kamar baka ganniba?"
  "Waye yakamata yafara yiwa wani magana da zakazo katakurani Ina aikin gabana"
  "hmm yayi zuwa nayi na tambayeka saikuma na sameka kana waya"
  "Uhmm Ina jinka"
"Wai ita wannan yarinyar menene alakanta da Khadija?"
Kallonshi yayi cikin mamaki sannan yace
"Wacce yarinya fa"
  Yatsina fuska yayi tare da hade Rai yace
"Banason wulakanci nasan kana sane da wadda nake nufi shine zakayimin halinku na Yan Nigeria"
  "Yazaka cemin wani waccen yarinyar ninasan wani waccan"
  Tsaki yayi sannan yace
  "Meyene sunanta Ni bansaniba wannan mara kunyar da nagani a gidansu khadijan ka Mana ranar nan Mai manyan idanu"
Murmushi yayi don yagane inda abokin nasa ya dosa don haka ya gayara zama tare da kafeshi da idanu yace

  " Wai Deenah kake nufi?"
"Oho Ni Ina nawani San sunanta" Amma acikin zuciyarshi tunani yake lallaima anciwa sunansa mutunci kawai, ama rasa sunan da za'a dunga kiranta dashi sai Deenah l.....
Katseshi yayi wajen cewa,
  "Ai gashinan nafada maka don haka sai Adena cemata yarinya"
"Ai wlh ko Ina za'aje bazan Dena cemata yarinya bah donma kaji"
Banza yayi dashi kamar baijiba,

Tashi yayi yabar office din ransa abace don bakaramin batamai Rai yayiba kilama ba sunan yarinyar kenanba zaiwani ce sunanta haka,

  Yana shiga office ya tadda wayanshi na ringing don haka y karasa da sauri ya dauka ganin Mai Kiran yasa jikinsa sanyi dady ne cikin sanyin jiki yadauka tare da karawa a kunne yayi sallama,
  Can bagaran dady ko amsa sallmar baiyiba yace
  "Saifudeen maza kazo gida inason ganinka yanzun Nan"
Cikin sanyin murya ya amsa da to,

Fitowa yayi ko office din Aminin nasa Bai komaba yayi wajen da yake yin parking din motarshi
  Shiga yayi yakunnata tare dayin waje,
  Cikin kankanin lokaci ya karasa gida Yana zuwa yaga motar dady tsaye a gefe shima Parker tashin yayi tare d sakkowa yashiga falon momy,
  Da sallama ya shiga amsawa sukayi kaninsane zaune a falon sai momy da Kuma haisar yaron mus'ab kenan kaninsa,
  Zama yayi kusa da momy Yana gaidata,
Ko kallon inda take batayiba ta amsa,
  Mus'ab ne ya gaidashi ya amsa Yana tambayarshi ya mamanshi murmushi yayi yace
"Tanacan tana rigima yau batajin dadi"
"Ayyah Allah sarki meke damunta?"
"Zazzabi take fama dashi sai kashin hakori"
"Ayyah Allah ya bata lafiya" ameen ya amsa sannan ya juya ta kalli momy yace
"Momy dady da?"
"Yana dakinsa"
Mikewa yayi yanawa haidar wasa yawuce shiga part din dady yayi a falo ya sameshi zaune Yana duba wasu takardu xama yayi tare da gaidashi ciki ciki ya amsa sannan yaci gaba da abinda yakeyi zuwa can ya juyo yayi gyaran murya yace.



*By*

*Deejah (UMMU FU'AD & AFNAN)*

*Allah kasa mudace duniya da lahira*😭

KOMAI NUFIN ALLAH NEDonde viven las historias. Descúbrelo ahora