7

40 6 4
                                    

Ta sha bugu kam saboda shegen bakin ta, amma pa bakin be mutu bah!.
Ehe!.

A Gaggauce suka gama shirin su ita da Murja suka yi hanyar madafa aka zuba musu funkasau ɗin da aka dafa sai suka koma ɗakin su suka ajiye da zummar idan sun dawo zasu ci gudun kar suyi latti. Suna ajiye wa sukayi bangaren Sarki. Sun ɗan yi tafiya kam ba laifi ahakan ma da tambaye tambaye kapin su isa.
Sashen Me martaba yapi kowane sashe kyau a kap cikin Masarautar tınba idan ka shiga cikin ba, tun daga farkon sashen suke kalle kalle har suka karasa ciki.

Suna zuwa suka tarad da jakadiya tana hakimce akan wata kujera se kace itace Sarkin sai saka bayi aiki take yi, idan kayi ɗan slight mistake kadan sai ta daka maka tsawa, abu kuma gashi nan a gefen ta amma sai ta kira wata daga çan uwa duniya ta miko mata. Da yake kowa da portion ɗin sa sai aikin ya zamto baya bawa Kowa wuya, Kuma ma Me martaba be yadda ana azabtar da bayi ba
Shiyasa ma wani lokacin da azahar zaka ga bayi sun gama Ayyukan su sai na maraice kuma su sake dawowa.
Sai kuma da daddare bayan isha su kan tafi makaranta inda ake koya musu karatun Allo, Ajami da dai sauransu amma ba ko wace rana ba.

"Kuzo nan, yaya sunan ku?
Jakadiya ta tambaye su kamar ba ita bace aka dake su a gaban ta ba jiya, ko ta sa baki, Gata dai dattijuwa amma sai shegen kwainane
Hafsa ce ta fara fadan sunan ta sannan Murja
"Daman yanzu nake cewa su Laure suzo sudauki abin nan sukai sashen Fulani amma tunda ga ku nan, kuma ba'a baku aikin ku ba sai ku dauka ku kai, kar ku jima pah?"!.
"Tohm ranki ya dade" suka fada a tare suna ɗan russuna mata cike da tsantar biyayya
Aiko Jakadiya ta saki murmushi domin tana son ana girmama ta, har cewa take ''zamu shirya da yaran nan'' a zuciyarta
Ɗauka sukayi suka wuce, buhu ne amma basu san meye a ciki ba

Sashen Sarauniya Fulani nada matukar kyau shima kuma a kusan na me martaban yake shiyasa basu sha wahalan dakon buhun ba.

"Kai ina zaku je?" Bafaden da yake gadin gate ɗin shiga sashen Fulanin ya tambaya da wata razananniyar kara
Ta tsorata sosai pah amma being the Hafsat she is, sai tace masa "ina ruwanka da inda zamu kai idon ka baya ganin aiko mu aka yi ne?
Ashe ran maza ya ɓaci aiko ya sungumi lafceciyar bulalar sa da nufin ya dake ta sai aka rike hannun sa
Dukkannin mu muka juya dan ganin waye da wannan ɗanyen aikin
"Ranka ya dade?"😲
Bafaden ya fada a tsorace

Murja da sauran fadawan da suka ga waye ne sai suma suka tsugunna alamun girmamawa.
Hafsah kuma tana ganin sa ranta ya ɓaci, duk da tsinkewar da zuciyar ta yayi sai gabobin jikin ta suka yaudare ta suka ƙi tsugunnawa su girmama sa, baza ta taɓa manta mutumin da ya sa ta a cikin wannan kangin bautar ba, kawai sai ta saka idon ta cikin nashi bata ko ƙiftawa, wannan shi ya hargitsa Yarima, dan gani ɗaya yayi mata yaji ya tsaneta,

Nan take ya wafce bulalan hannun bafaden ya shiga tafkar ta kaman ya samu jaki.
Sai da hannun sa ya gaji kafin ya kyale ta, amma abinda ya ƙara ɓata masa rai shine duk dukan ta da yake yi ba tayi hawaye ba kuma har yanzu idonta a cikin nashi yake

"Karbi tsumagiyar nan Barau kayi ta tafkar ta har sai ta dena numfashi."
Ya fada a fusace, tare da barin wurin gaba ɗaya
Aiko nan take Barau ya karbi tsumagiyar ya shiga tafkar ta daman yaji haushin rashin ɗa'ar da ta masa nan yaci gaba daga inda Yariman ya tsaya.

____________________

Da Malam Sule me rini ya koma gida sai ya zayyane musu abinda ya faru suka yi ta Sallallami

Su Kulu baki ya mutu dan ɗan kananu - kananun maganganun sun nan shiru kake ji, kamar gidan makoki.
A haka aka zo akayi bikin Lawan da su Garzali
Su Garzali matan su daman acan Gomben suka samo su
Sai Lawan ne da yanzu yake sana'ar rini ne ya auri Salamatu (wata kawar su Hafsa da su Azima)
Su Hafsa kuma Malam Sule me rini yace su ukun su ze hada auren su idan Hafsa ta dawo, kapinnan yace su ƙara shiga hankalin su su fidda miji nan da dawowar Hafsan.

Bayan wasu kwanaki kowa ya ware ya fara harkan gabansa
Malam Sule me rini kuma ya koma bakin aikin sa ya bar Lawan da Kula da gida
Wannan kenan.

____________________

Saura mako biyu da rabi ayi gasar ta Horse race da ma wasu wasanni kala kala da ya shafi sarauta hakan yasa aka fara shirye shiryen tun da wuri, wanda ya kama yau kwanan Hafsa talatin cif cif da zuwan ta cikin masarautar
Kwana goma sha shida da zuwan mahaifinta da kawun ta, kwana goma sha hudu da tasha bugu a gurin Yarima da Barau
Sauran mata kwana sittin kenan kan Galadima yasa baki a sallame ta
Ta sha wahala sosai pah domin ciccibar ta aka yi aka kaita dakin magani bayan dukan da aka mata
Jinyan kwana biyu kacal tayi, suka koma bakin aikin su inda Murja tana goge gogen dakin hutawar me martaba, Hafsa kuma gyaran ɗakin sa, sai dai dakin me martaba ana sa ido sosai shiyasa duk sanda za'a gyara shi aka idon jakadiya ne.

Yau ya kasance daya daga cikin ranakun da bayi ke fita koyon karatu, Bayan kowa ya gama aikinsa na safe da marece, kowa yayi Sallan Maghrib da Isha sai aka hallara zuwa makarantar bayin, wanda yake da kwakkwaran uzuri kamar rashin lafiya zai iya zama a sashen bayin sai wanda suka je su bada shaidar rashin lafiyar tasa
Makaranta ce babba sosai me dauke da azuzuwa dayawa a ciki wanda yake kunshe da bayi maza da mata, ajin yara ƙanana maza da mata ne a haɗe, na manya kuma maza daban mata daban, tsofaffi da dattijai ma da nasu, mazansu da kuma matansu

A cikin masarautar daman makarantu biyu ne, na Bayi da na ya'yan attajiri i.e The royals

Hafsa ne da Murja na gano sun fito daga cikin sashen bayi a makare, sai hanzari suke yi su isa, kafar Murja kamar zata cire tsabar sauri sai chilla su take kamar zasu tsinke
Suna isa makarantar sukayi sanɗa sanɗa za su shige aji sai ji sukayi shugabar bayi ta fisgo su
Zare ido sukayi suna
''Mama dan Allah ki taimake mu kiyi mana rai''

''Naji, amma kuyi sauri kubi wannan bafaden'' sai ta nuna musu Barau da yake ta wani ciccikowa.
"Ku hanzar ta jakadiyar Sarki ke jiran ku"
Maganar shugabar bayi kenan

Nan suka shiga bin bayan Barau, ''dube shi basamuden banza'' Hafsa ke maganar a ranta, tare da yatsina fuska, Murja ta daga mata gira alamar tambaya, sai tace babu

Shiko gogan sai uban sauri yake, wanda idan ya jefa ƙafarsa daya shine su sun jefa uku tsabar saurin sa, nan da nan suka isa kuwa.

A bakin sashen Fulani suka same ta a tsaye tace su biyo bayanta
suna shirin gaidata amma ko takansu bata bi ba, sai abin ya basu mamaki
Har suka isa ba wanda yama wani magana sai zare idan da su keyi

Suna shiga sashen Fulani suka ga hankalin ta a matukar tashe, gefen ta Kilishi ce tana murmushin mugunta.
Yaune rana na farko da suka taba kallon matan Sarki, gaskiya matan sa kyawawa ne musamman ma wanda suka ga hankalin ta a tashe yake sosai, fara ce sosai kuma kyakkyawa dan har tafi dayar kyau ma, nan Hafsa ta fara ƙare mata kallo, Wait!
"😳😳Wlh matan nan da wannan hamshaqin mugun nan take kama. Tabbas itace mahaifiyarsa". Bata gama maganar zucin ta ba taji ance;

"Ku kwashi kayan nan kukai sashen Yarima babba"
Muryar Jakadiyar sashen kenan da ya karade dakin

Nan suka tsugunna a tsanake suka kwashi manyan kwanukan dake a cikin wasu kwando guda biyu,
"Har kwandon za ku hada".
Jakadiya's voice echoed again

Kilishi ce tayi wani mummunan murmushi tana sake sake a ranta
Ita pah dole ne a cikin yayanta tagwayen nan daya yayi sarauta bata damu koma waye bane amma dole de a cikin su daya ne ze zama, shiyasa ma ta fara gudanar da aikin ta yau domin Boka Kafoor ya tabbatar mata da jinin ta ne dole ze mulki wannan masarautar, amman bata yi zaton har aikin nan ze fara tasiri akan sa ba yau din da wurwuri haka, tafi san sai anyi gasar nan da za ayi nan kusa, kimarsu ya dada karuwa tukun, Tabbas a cikin yaranta maza Hayatu yapi Shamsu nutsuwa amma ba hakan ne yake nupin idan samun mulkin yana kan Shamsu ne ta hana shi ba
Ehh ita koma waye ne a cikin su ya samu muddin zata kunyatar da Waziri da ita kanta Fulanin, toh bata da damuwa
Nace tohh pah🙄😆

Alhamdulillah
Let's meet in the next chapter
Fadrees Bello❤️.
09020588802 chat me on Whatsapp

Yariman Hafsa.Where stories live. Discover now