10

38 4 0
                                    

Not edited.

Daga kai Hafsa tayi tana karewa dakin kallo, daki ne me girman gaske dan yayi ukun dakin su na can gidan su ma a girma, tabe tabe ta fara yi a ciki ko Allah ze sa ta samu abinci, bata ga komai ba tayi shirin juyawa da sauri dan gaskiya tayo babban kasada da ta sako kafarta a cikin wannan dakin, amma se ta tuna aiki zata yi ai nan ta fara neman abinda zata sa a cikin ta, kan dardumar da suka shimfida musu jiya da daddare ita da Murja idon ta ya fada a kai, nan take jiki na kyarma ta karasa wurin.

An tattare gurin tsaf an kwashe kwanukan jiya se wasu ta gani sabbi a gun, nan ta fara bude ko wanne, idan ta ne ya hau kan dafaffiyar kaza, a take ta hadiye muguwar yawu, haka tana ji tana gani ta rupe, duk abinda ta bude se ta ga yafi karfin ta seta rupe shi, daga karshe har ta yanke shawarar tashi, ta ga baza ta iya ba nan ta bude kwanon soyayyar awara da kwai, ko takan miyar bata bi ba ta fara afka su izuwa bakin ta, hannu baka hannu kwarya, tasss ta cinye ta kora da wani ruwa me zaki
Tashi tayi tsaye nan taji ta dawo garau, kwanon ta dauke tayi waje dashi ta hango wani bafade ta tambaye sa ina ne madafar sashen Yarima ya nuna mata ta kai ta dauraye taje ta ajje a cikin kwanukan madafar sannan ta koma dakin ta fara gyara ko ina tsaf, taje ta wanke banɗaki ta shiga dakin hutawar shi ta gyara shi shima, nan ta samu wuri a gun ta kwanta se bacci.

_______________

Bayan su Yarima sunje sun miqa gaisuwa a fada, nan take suka wuce filin polon su suka fara training shi da su Sulaiman da su Shamsu, can dai zuwa azahar yaga yunwa tana neman halaka shi, gashi be ci abincin safe ba, ya dai sa an kai mishi, nan yace musu suje su huta zuwa yamma su sake dawowa, a take kuwa sukayi haramar tafiya, sashen mahaifiyar Yarima naga sun nufa, Seda aka musu iso kapın suka shiga suka duqa suna kwasan gaisuwa
Bayan sun gama su Hayatu suka mata sallama suka fice zasu gurin mahaifiyar su daman ance tana neman su

Fulani ce ta dubi Yarima cike da so da kauna tace

"Ya jikin abokin naka Sulaiman"?
"Da sauki ranki ya dade yanzu ma daga filin polo muke munje training"
Sulaiman din ya bata amsa
"Ku dai kun ki kuyi aure, Allah ya sa Me Martaba ya zaba muku mata in yaso wani shekarar ya zamto mun zamo kakanni"
Fulani ta karashe maganar ta tana kallon Yariman
Gogan kuma ya gimtse fuska, shi shiyasa sam be san zuwa gun Fulani dan da yazo zata kama mishi zancen aure
Shi tukunna ma be yadda da so ba, sannan shi dai gaskiya a iyaka rayuwar shi be taba soyayya ba, ba ma shi da wannan time din, anso ayi mishi hadi da ya'yan sarakuna amma yaqi bada hadin kai, kuma ya lura yawancin su kyan shi ne yake fusgar su, a ganin shi soyayya bata lokaci ne da kuma wani nauyi da ka dora ma kanka.

Yana cikin wannan tunanin suka ji sallamar Bilkisu,
Yaya Sulaiman sannu da zuwa, Yaya Barkan ka da warhaka.
Ya dai ji Sulaiman ya amsa mata har yana tsokanan ta, shikam yunwan da yake ji ma baze barsa yayi magana ba

Alama Fulani ta ma bayin ta da su kawo ma su Yarima abinci, ba bata lokaci se ka abinci a jere a gaban su, nan suka hau ci dan shi kan shi Sulaiman din yunwa yake ji, tunanin Yarima tunda yanzu yanar abinci a sashen sa, awaran kawai zeci, tunda shine favorite nasa in ya so se ya bawa bayin sa sauran kamar dai yadda ya saba.
Bilkisu kuwa se zuba take tayi, daga karshe ce mata yayi in baza tayi shiru ba zata iya tafiya, Fulani ko se dariya take

Shine pa suka samu salama, can dai Sulaiman yace mata
"Ina kawar ki ne?, nipa tun jiya ban sa ta a ido ba"
Zare ido tayi cikin mamaki tace "kai yaya Sulaiman kuna gida daya kace baka sata a ido ba tun jiya"? Nan ta saki baki se zuba take

Kawai se gani suka yi ta miqe ta fita bakin ta a zumbure, ashe da ido Yarima ya mata alama da ta fita.
Suna gamawa suka tafi masallaci daga nan suka wuce sashen Yariman

Da sallama a bakin shi ya shiga sashen, se kuma yaji shiru ba kamar yadda ya saba idan ya shigo masu aikin sa su fara gaishe shi ba, nan de ya karasa ciki Sulaiman na biye dashi, shima yana mamakin shirun da yaji
Suna shiga tsakiyar dakin shaqatawar suka hango Hajiya Hafsa a sheme tana kwasar bacci, tayi dai dai da kafafu daya yana kallon gabas daya yamma, kai babu dankwali gashi ya rupe mata fuskan kamar wata mahaukaciya, zani ya taho cinya, ba'a san a wacce duniya ake ba, tsabar baccin ya mata dadi har gyara kwanciya take, Me Sulaiman zeyi in ba dariya ba, shi kuma Yarima ya qule ya qule, wato ita ba aiki taxo yi ba, bacci taxo yi kenan, bari ya koya mata hankali.
Ƙafa ya sa, ya haure mata ƙafan, ita kuma a take ta tashi a matukar xafafe tana me kuntuma wani mugun ashar.
Idon da suka hada ne yasa taja bakin ta shiru tana hararar ƙasa.

________________

(Recap)
Hafsa ce kwance tana mafarkin gata a gida, Mama ta aike ta taje ta siyo musu kosai a gun mama lantana, ita kuma tace wlh baza suci na Mama lantana ba, bayan ta gama tofe yawun ta a cikin kullin wlh baze yiwu ba sede Jamila kije can rumfar iya me kosai ki siyo mana, da Mama taga haka se ta kwace kudin ta wai ta fasa siya musu kosan, ihu suka ji a waje sukayi waje da gudu, wai Sega su dije suna dambe ita da Azima, ita kuma Hafsa taje tana ta ziga su tana dariya, dambe kuwa ya kara rikicewa an kasa raba su, mama ne ta taho da mahuci ta kwalawa Hafsan daidai da taji saukan shuri akan kafar ta kenan, shine pa ta tashi tana zambaɗa ashar
Se kuma tayi gamo, bakin ta yayi laqwas tayi shiru tana hararar ƙasa
Shi kuma mutuwan tsaye yayi.

See you in the next Chappy
Vote oo.

You've reached the end of published parts.

⏰ Last updated: Mar 24 ⏰

Add this story to your Library to get notified about new parts!

Yariman Hafsa.Where stories live. Discover now