WG-04

553 32 2
                                    

Daga inda take kwance gindin ruwan ta hango yara suna hawan bishiya suna tsinkar yayan itatuwanta, kamar an cikareta haka ta tashi tsaye da sauri tana kallonsu, daman can babu abun da ta aje a ranta sai keta da son azabtarwa, itacen dake kusa da ita ta kama ta hau fir sai gata ta dale kan itacecen haka ta rika bin itacen tana sauka saman wannan ta hau wannan har ta isa gurin da yaransu, bata tsaya yi musu cewa su sauko ko su daina ba, saboda tana da hurumin hana su domin itacen ba na gidansu ba ne, ko da na gidansu ne bata da wannan damar balle na wajen gidan.
Sai da ta kalli yaron da ta fi girma ta turashi da karfi ya fadi kasa, sai ta fara dariyar mugunta haikam, sauran yaran na ganin haka suka sauka daga kan itatuwan suka ranta a ana kare suka bar yaron daya fado kasa yana ta ihu da neman ceto. Mikewa ta yi tsaye saman itacen ta tsinki ganyensa da wani gafe na reshen itacen ta fado tun daga kan itacen zuwa kasa ta tsaye, ta nada itacen da ganyen ta dora a kanta sannan ta dauki fruit din daya fado ta fara ci tana yamutsa fuska saboda tsami, hango mutane tafe ya saka ta gudu ta boye a bayan wasu itatuwan tana leke har aka dauke yaron, sannan ta zauna a gurin tana ta dariya.
  Daga zama sai gata kwance ta daga kafafuwanta sama ta jingina su da itacen tana kallon sama, labarin da Eid ya bata take tunawa, akwai wasu mutane masu abun hawa da rayuwa da ba irin na su ba, abincinsu da yarensu da addininsu ba irin nata ba.

“Kuma suna jin dadi rayuwa?”

Ta tambayi kanta da yaren da shi aka haife ta kuma shi ta iya, zuciyarta ta raya mata babu wani jindadi ga wanda yake rayuwar da ba irin ta su ba, a gurinta hawan tsaunuka da itace da manyan duwatsu ya fi komai dadi, ka shiga lambu ka tsinki abun kake so ka ci ya fi komai saka nishadi.

“Outarrr”

Ta maimaita tana dariyar sunan da ya fada na abun hawansu Mota take kokarin iyawa. Kamar daga sama ta ji muryar Eid, da sauri ta tashi zaune tana kallonsa har ya karaso. Tada ita yayi tsaye ta cire mata ganyen data saka a kanta ta jefar ya rike kafadunta.

“Me kika aikata?”

“Ban yi komai ba”

Ta bude hannayensa zata tafi ta dauko ganyen ya riketa.

“Sarki yace a zo da ke, kin jefar da yaro”

A take ta saka dariya, duk kuwa da kasancewar bata ga wasa a fuskarsa ba, sai dai ta san ba a yau ta saba irin wannan ba kuma kowa be tana ce mata komai ba, sai dai Eid yana yawan nuna mata abun da take yi ba shi da kyau, yana daga cikin dalilin da ya saka bata da kawaye kuma kananan yara basa matsawa kusa da ita.

“Na sha fada miki ki daina wannan halin”

“Su suka ja ni”

“Karya kike yi, ba za su ja ki haka nan kawai ba”

A karo na biyu ta buge masa hannu saboda ya karyatata, sai ya sake rike kafadarta gam.

“Muje Sarki yana son ganinki”

Ya saki kafadar ya rika hannunta ya ja kamar wata kuya yana gaba tana baya har suka isa cikin fadar, tsananin girmamawa da ganin kimar sarki ko yayan mulki a garin ba a hada ido da su sai idan ta kama dole, idan za a gaishesu kuma sai an risina. Eid ya gaishe da sarkin dake zaune tare da jama'arsa sannan Waira ta risina ita ma ta kwashi gaisuwa, Sarkin dake cike da far'a da murnar bikin da aka yi ya kalli Waira da idonta ke kasa hannunta ke rike cikin na Eid yayi murmushi.

“Ranar yau rana ce mai girma da muhimmanci a garemu, be kamata ace kin kuntatawa wani ba, ba wannan ne karo na farko da aka kawo min kararki ba, amman wannan ne karo na farko da ya kamata na gargade ki, kuma ya yafe miki, kar ki yarda a sake kawo kararki akan kin zalinci wani, zan yafe miki iya na yau kawai saboda albarkar ranar yau da kuma kasancewar ban taba gargadin ki ba sai a yau, ke ta dabam ce a cikin yara sa'aninki Waira, matsayinki da na su ba iri daya ba ne, kina jiran wani matsayi da su har su mutu ba za su iya hawansa ba, ya kamata ki banbanta kanki da sauran yara”

WANI GARIWhere stories live. Discover now