Page 25

5.3K 229 1
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_

                       *KWARATA*
      _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_

_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

                         &

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*

🅿 ------ 25

           Tunda suka shiga sukayi ta kwarara sallama shiru babu wadda ya amsa , Hafsa itace ta basu ƙwarin guiwa cewa kawai su shiga palo , gaba ɗayansu sunkayi na'am da wannan shawara dan haka suka ɗinguma suka shiga cikin palon tare dayin sallama...

       Daga cikin bedroom Asma'u ta amsa sallamar tare da cewa ku zauna ina zuwa , murmushi Amisty tayi tare da cewa ko munzo da wuri ne mai gidan bai fita ba ? Daga cikin ɗaki Asma'u tace ya fita amma yana dawowa babu jimawa wanka dai na fito ina ƙoƙarin saka kayana !

      Wani irin ajiyar zuciya Hafsa ta sauke tare da cewa zanyi fitsari ta faɗi maganar cikin sigar kwartanci ma'ana tayi maganar a sakantace tare da kasalanci yanayin maganar dai sune kaɗai suka san fassarata ,

      Akwai toilet a nan waje inji Asma'u tare da ƙoƙarin fitowa daga bedroom in dan nunawa Hafsa inda toilet in yake , towel ne ɗaure a jikinta ko guiwa bai kawo ba saboda tana da wani irin kugu ne shi yasa towel in ya haye saman ɗuwawunta shi ya hana towel in saukowa sosai '

        Idanuwa Amisty ta zaro sosai kamar zasu faɗo ƙasa tare da jan wani irin gauron numfashi sannan tace babu toilet a bedroom inki ne ? Ta faɗi maganar kamar numfashinta zai ɗauke , murmushi Asma'u tayi tare da cewa akwai bara dai ta shiga na wajen !

     A ƙofar palo sukaci karo da mijin Asma'u , tunda ya ganta ya haɗe girar sama da ƙasa tare da cewa wannan wane irin sakarci ne ? Ke wawiyar inace zaki fito haka ..... ?

         Cikin biyayya Asma'u tace ai ba kowa gidan ne duk mata ne , matan banza matan wofi da Allah wuce kije ki saka hijabi malama , yayi maganar cikin kausassar murya tare da ƙara ɓata rai kamar zai daki Asma'u ,

        Simi simi Asma'u ta wuce ta koma ciki , saida ta shige sannan yabi bayanta , a palo ya samu su Amisty zaune riɗi² ,  duk gaishe shi sukayi amma babu wacce ya kalla bare su saka ran zai ansa gaisuwar wata daga cikinsu ya wuce ciki abunshi....

     A bedroom kuwa faɗa ya rufe Asma'u dashi tare da cewa ina kika samo wa'anan karuwan ? Kai ƙasa ² tace maƙontanmu ne , zama yayi a gefen gado tare da ci gaba da cewa gaskiya ni bana so suna zuwa gidan nan kima taka musu burki kar na sake ganin kowa na faɗa miki ,

      Cikin yanayin damuwa Asma'u tace haba Baban Abdul babu daɗi na ce su daina zuwa , cikin ɗaga murya yace tou wallahi idan baki musu magana ba ni da kaina zan musu magana zance kar na sake ganin ƙafar ko wace a gidan nan , daga shiga bayi kilbibi zai fara yaɗuwa , miƙewa yayi tare da cewa tunda tsoronsu kikeji ni bara inje in faɗa musu...

      Da sauri su Amisty suka miƙe kafin mijin Asma'u ya fito tuni sun fice daga gidan , koda ya fito palo bai samesu ba , dan haka ya koma yana cewa sun rufawa kansu asiri da suka gudu , ita kuwa Asma'u bataji daɗi ba saisu Amisty su gani kamar itace tasa mijinta ya tozarta su kuma tabbas nasan sunji kana faɗa irin haka babu daɗi...

      Cikin ƙara faɗaɗa faɗanshi yace ai dama bana so suji daɗin kuma idan na sake ganinsu gidan nan saina ci mutuncinsu , Asma'u tace tou shikenan ka haɗa hadani kaci mutunci gaba ɗaya , tou zanci hada naki ki barsu suci gaba da zuwa gidan nan kiga yadda zamu ƙare dani dake...

KWARATA...Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon