Page 42

6.2K 261 11
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_

                       *KWARATA*
      _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_

_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

                         &

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*

🅿 ------ 42

     *_AHUMAGGAH yadda kika fara lafiya ubangiji yasa ki kammala lafiya , ku nemi naku karku bari ya wuceku daga alƙamin SURAYYAHMS haziƙar marubuciya mai tafiya dai² da zamani yana nan yazo..._*

 
      Kallon wane yaro nayi nace kai muje ƙofar gida kaji , na faɗi maganar ina nufar hanyar fita , riƙoni Amisty tay ta baya tana cewa babu wani wajen da zakije anan zamu ci uwarki , ban kalleta ba na kalli inda ta riƙeni nace sakemin hijabi , Hafsa tace baza'a saki ba kina nufin mu zaki ɗauka wasu ƙolaye mu barki kuma , murmushi nayi na kalli Hafsa nace sakarar banza ba ƙolaye ake cewa ba kuzo muje ƙofar gida , saboda bana so ayi wulaƙancin a gaban Babana da kuma sauran jama'ar dake gidan gani na ma kawai yasa sun kora "ya "yansu ina kuma ga anyi wannan maganar a gabansu , duk a zuciyata nayi wannan nazarin ....

      Babana ya karkato cikin yanayin jin jiki yace Uwar masu gida me ya faru ne ? Nace ba komai Babana , a kadarance Amisty ta kalleshi tace ai kasani , a wahalce ya kalleta yace me na sani ne Amina ? Nace Baba da Allah ya isa haka kayi bacci abun ka kada a ruwa ai sarki ne kaja bakinka kawai kayi shiru domin ni wutar kara ce ba'a kwana dani ba saidai idan ba bacci ake ba !

      Mamana..... Ya faɗa tare da lumshe idanuwan shi yace mene ne ? Kallonshi nayi cikin ɓacin rai nace wutar da aka daɗe da kashewa ni kuma nake so yanzu ta ruru , cikin hayaga ga , nace ɗaukar fansa da ramuwar gayya a cikin jininka yake Babana , baka gada ba ni kuma na gada ɗan koyo da ɗan gado dukansu idan suka tashi sai sun zarta ,

     Na rantse da ubangiji da ya bani aron lumfashi da rayuwa dawowa ta sai ta zame ma kowa tashin hankali saina firgita kowa saina jinyata duk wanda ya shigo rayuwata , wallahi ׳ Amisty da Hafsa kun sake toƙalowa kanku masifa idan baku kiyayeni ba uwar kowa a cikinkun nan , na nuna su da ɗan yatsa na jinjinashi nace kuma nayi rantsuwa...

Da sauri Hafsa ta kalli Amisty suka kalli juna cikin firgici , komawa nayi na zauna tare da cewa har kun firgita kenan ko ? Jinjina kaina nayi tare da cewa baku ga komai ba furtawa kaɗai nayi kuma ban faɗa muku abinda zan aikata ba amma tabbas wani abu zai faru , kallon wane yaro nayi nace kai bani abinci kaji , gabana ya ajiye abinci nace muci shi tare , babu ɓata lokaci yasa hannu mukaci gaba dacin abinci ,

      Kallo Babana ya bini dashi na wani lokaci sannan ya kalli Amisty yace mi ya haɗaku da Uwar masu gida ? Amisty tayi shiru tou maganar dai bata faɗuwa da kunya tace tsiraicin Babanta na ɗauko , tayi shiru ta kasa magana , lashe hannuna nayi tare da cewa bara kaji abinda ya haɗamu Babana ,

     Kafin in ɗago su Amisty sunyi layar ɓata domin dai bansan ta inda sukabi suka fice ba , murmushi Babana yayi mai nuni da yana alfahari dani , kallon wane yaro nayi nace jeka idan Allah ya kaimu jibi ka dawo ina neman ka , godiya yayi ya fice daga gidan , ni kuma ɗakina na nufa ina zuwa na cire kayana , alwallah nayo nazo nayi sallah azahar har saida nayi la'asar sannan na tashi ,

     Komai na ɗakina yana nan yanda yake babu abinda aka taɓa har kuɗin dana sata a jakar Amisty duk suna nan , wanka nayi na saka kaya na fice daga gidan , a napep naje gidan su Mamy wacce muka haɗu da ita a wurin saloon , ban sameta gida ba , saidai nabar saƙo idan ta dawo ace mata Sultana tazo mu haɗu gidanmu jibi idan Allah ya kaimu ,

KWARATA...Where stories live. Discover now