Page 69

5.8K 210 1
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_

                       *KWARATA*
      _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_

_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

                         &

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*

🅿 ------ 69

           Hihihihihihi yayi wannan munafikar dariya da bana so , saitin wuyana ya ɗora wuƙar dai² maƙoshina lokaci guda na ɗauke numfashina zufa ta ketomin hawaye suka ci gaba da gangarowa nabi Bello da kallo , dariyar ya sakeyi tare da jan majina , yace kin tuna kika tuɓeni kika ɗaukeni video ? Ka turo da dubu ɗari biyar idan ba haka ba zan watsa su a yanar giza gizo , yayi irin magana na , dakel na haɗi yawun bakina cikin tsoro nace wai me kake so da rayuwata ne ?

      Bana buƙatar komai a halin yanzu sai mutuwarki , bara in faɗa miki abinda kika kasa sani nine nan na kashe Binna da hannuna , kuma nine na toshe miki kwalwa na maidake kidahumar ƙarfi da yaji nine na haɗa Binna da Hafsa da Amisty suka zama karuwanshi , haka yake jerasu a layi ya hau akan ɗaya ya sauka ya hau ɗaya , nine nan na shirya komai ta yadda ya faɗa wasan caca shine kawai zai fita a caca nayi na mayar dashi ya ƙiya saboda kawai yayi miki alƙawari ya daina yaso ya lalatamin tsarina ne ni kuma kawai na kashe banza , to me Babana yayi maka haka da zafi ? Ke matar da nake so ya maida ita zawara a ranar da nake farin ciki zan shiga daga ciki , da farko na barshi ta tafi Yayan Babanki ya zugani na dawo dashi ni kuma na hura wutar ɗaukar fansa a zuciya , zan gama da matsalar Binna dake na koma wurin ɗayan ɗan iskan saina ƙare kaf ahalinku dan bana buƙatar ganin jinin Binna a saman doron ƙasa , kauda kaina nayi gefe ɗaya ina wani irin gumji nace kaine ka kashemin min Babana......? Nine na kashe shi ko in nuna miki irin zamiyar da kikayi a jikin gawarshi ne ? Yadda nayi ya nunamin kina cewa wayyo Babana karka ka tafi ka barni tashi Babana baza ka mutu ba gani nazo , buɗe idonka kar kayi bacci uwar masu gida wayyo Babana yi murmushi hihihihihi yasha majina jeki....... Ya faɗa tare da so kamin wuƙa a kafaɗata wanda ba haka yaso ba zuciyata ya saita kuma a samanta yaso wuƙar ya shiga...

     Wani irin ihu nayi tare da haɗa hannayena wuri ɗaya 🙏🏻idona yana tsiyayyar da hawaye nace na roƙeka karka kasheni , wata "yar iskar rawa yayi da ƙugunshi yace ke kina tunanin zan barki ki rayu bayan nace miki nine na kashe Binna ? Cikin kuka nace ai banji ba , hihihihi yaja majina ƙazamin banza yace sai kin mutu......

     Ci gaba yayi da yankata ina gocewa yanka 3 yayi min a kafaɗa wuyana da bayana , ta ƙasan sa na sulɓe nayi waje da gudu ina ihu , biyoni yayi da wuƙar tsabar toshewar basira yana saina hallakaki nine ajalinki wallahi baki wuce yau sai kin mutu , masu ɗinki da suka fito suma tuni sun tara taron jama'a dan a kawomin taimako , jini sai zuba yakeyi a jikina ina gudu Bello yana bina , da gudu na shigo titi zan tsallaka road in da gidan Dikko yake fitowarshi kenan zai fita , ina dafe wuyana na fara ɗaga hannu dan motocin suna san su wucemu ne , wani irin ihu nayi nace Dikkkkkkkkow na tun kari motocin da gudu kai tsaye , wani irin burki Ashiru ya taka ni kuma na juya dan jin maganar Sultan shine fa Bello ya samu damar sokamin wuƙa a ciki yana cewa saina kashe ki , wani irin yunƙurin amai nayi kamar raina zai fita na ɗagawa Sultan hannu dan bana iya magana....

Da gudu Dikko ya fito daga cikin mota ya zaro idanuwanshi kamar zasu faɗo ƙasa yace me zan gani haka ? Shima Sultan da gudu ya nufo wurin , wani irin gurnani Dikko yayi cikin wata irin murya yace An mata , tare suka iso wurina dashi da Sultan , Sultan yana ƙoƙarin riƙeni Dikko yayi mishi wani irin halbi ya koma can baya wurin motarshi ya faɗi ƙasa , rumgumeni yayi a jikinshi ya riƙe hannu Bello tare dayi mishi wani irin kallo cikin kuka yace An mata me yasa haka ? Bana iya magana kwata² saboda ina tafiya wata rayuwa daban , cikin rawar murya yace riƙeni An mata riƙe Dikkonki ina tare dake babu abinda zai sameki riƙeni mana , ko motsin kirki bana iyawa Dikko kuwa cewa yakeyi daina kuka an mata ba gani nazo ba , yayi maganar cikin sigar tausayi.

KWARATA...Where stories live. Discover now