Page 66

8K 381 38
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_

                       *KWARATA*
      _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_

_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

                         &

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*

🅿 ------ 66

       Daga Bello har Dady duk tsoro ya kamasu kowa a ƙagare yake yaji abinda boka zai faɗa bayan sun kora masa bayani cewa sudai duk yadda za'ayi ya kashe Sultana har yanzu basu samu yarinyar ba , kuma a halin yanzu babu wanda yasan inda take ,

      Dariya boka yayi sosai sannan yace nace bazan iya kasheta ba , Dady yace me yasa ? Boka yace aljannun da nake tsafi dasu basa san mutum mai cika kamsus salawat dole sai yarinyar nan ta daina salloli biyar a rana kaɗai zasu iya kasheta , ba kuma zasu kasheta ba tana cikin jinin al'ada ba dole² sai ta daina sallah sannan kaɗai su iya kasheta.

       Dady yace zan baka miliyan ɗaya , girgiza kai boka yayi cewa bata ansuwa kuma bata ciwuwa kuje kawai kusan yadda zakuyi ku dakatar da ita daga sallolin dana faɗa idan ta daina ni kuma zansa aje a tsige mata wuya , cikin hayani ya ida maganar cewa ku tashi ku bani wuri......

      Daga Dady har Bello da sauri² suka fito daga wurin boka bayan sun fito ne Dady ya kalli Bello yace duk yadda za'ayi ka samo mana yarinyar nan mu kasheta da kanmu idan har ka samota zan baka zunzurutun kuɗi har naira miliyan 20 , murmushi Bello yayi ya kalli Dady a ranshi yace haba ai kafin Sultana ta mutu kaine mutum na farko da zan fara kashewa , yadda ka wulaƙantani a ofishin "yan sanda kana tunanin ka wulaƙanta banza.....?

Amma a fili sai yace zan iya Alhaji amma ba zanyi aiki bashi ba , Dady yace dama ka taɓamin aiki a bashi ne ? Bello yace har yanzu ina binka cikon kuɗin shiga rayuwar Binna da nayi tun muna matasa , ina binka kuɗin asirin da nayi masa ya shiga caca ya shiga harkar mata sannan kuma har yanzu kuɗin lalata rayuwar Sultana sisi ma baka bani ba ,

     Dady yace to wannan zan baka dai , Bello yace tou idan ka haɗo kan kuɗaɗen saika kawomin ni kuma a ranar zan shafe lissafin sunan ta a cikin jerin sunayen masu lumfashi a duniya , Dady yace karka damu zuwa ƙarshen satin nan zan baka , haka dai suka shiga mota suna tattaunawa....

     Auntyna ga wasu kayan mata na kawo miki suna da kyau sosai kuma zakiji daɗin amfani dasu masu kyau ne jarababbu ne , Mardiyya ce a gaban Jiddah take korata mata bayani akan kayan matan data haɗo take mata bayani cewa kinga wannan sunansa babu sauran kallo , wannan kuma rantse baki da kishiya , Jiddah tace ya rantse baki da kishiya.....?

       Murmushi Mardiyya tayi cikin kwantar dakai mai nuni da salon yaudara tace ai Aunty idan kikaje sayen maganin sai kinyi rantsuwa baki da kishiya ma sannan a siyar miki dashi , dan idan har kina da kishiya ba'a baki shi dan Yaya DK bazai sake zuwa wurin ta kullum yana tare dake manne kamar hanta da jini , dariya Jiddah tayi ta ɗauki maganin tace Mardiyya ina kika samominshi ne ?

     Mardiyya tace ni na samo miki shi a Banbaɗawa kuma Aunty da tsada na siyo shi fa , shi kuma babu sauran kallo Yaya baya sake kallon ko wace mace saike domin kece sarauniyar zuciyarshi , dariyar jin daɗi Jiddah tayi cewa kuma kamar kinsan aure zaiyi , wata irin faɗuwar gaba Mardiyya taji lokaci guda taji wutar ganinta ya ɗauke , Jiddah taci gaba da cewa ance ma Momy yana aiki gidanshi na goruba road wai acan zai ajiye matar , gidaje biyar ya siya ya haɗe yana tayi ma amarya gyara , amma Momy tace masa ko waye ya tsaya masa bazaiyi aure ba sai yace mata dama ai ba aure zaiyi ba , kuma da tace masa ance mata yana gyaran gida idan ba aure zaiyi ba me yasa yakeyi ? Shine yace mata masu gidajen ne kawai zasu siyar shine sukace da Allah ya siya shine fa ya siya.......!

KWARATA...Where stories live. Discover now