Page 88

9.8K 412 61
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_

                       *KWARATA*
      _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_

_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

                         &

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*

🅿 ------ 88

        *_Godiya mara iyaka zuwa gareku ,_* 👇🏻
*_HADIZA MATAWALLE..._*
*_RUKY    " " " " " "_*
*_FATY    "  " " " " "_*
*_ZEE      " " " " "_*
                     Ngode sosai ku huta gajiya Allah ya daɗa zuminchie...

    *_Gaisuwa marar iyaka zuwa gareki ZAINAB AHMAD KADUNA { Sheke } ina miki fatan alkairi tare da NA'IMA ABU KANKIYA..._*

     Tabbas wannan zance haka yake , Allah ya bawa Dikko lafiya ya ƙara soyayya a tsakaninku ya kuma ƙaro irinsu Papi hada Junior Dikko muzo musha suna , murmushi Sultana tayi amma batayi magana ba , saukowa nayi daga saman gadon ina ɗan gyarawa cewa ni zan wuce zan tara ƙarshen labarin a takardar labarin rayuwarki , godiya tayi min sosai mukayi sallama cikin mutunci da mutuntawa , itama Inna munyi sallama cikin mutuntawa na barsu lafiya nima zan tara muga ƙarshen labarin tare daku masoyan Sultana & Dikko ,

     Bayan Jamila ta tafi wanka na farayi tare da ɗoro alwallah dan magrib ya gabato , ina fitowa kayana na saka na shafa mai sama² da powder naci gaba da tattara kayan da Inna keyin parking zatayi tafiya zuwa Abuja ita da mijinta.

     Inna ce ta shigo ɗakin tana cewa wai ga wani Abbakar can yana miki sallama a waje , ba tare dana kalleta ba nace wane Abbakar kuma ? Abokin ɗan iskan yaron nan mana , murmushin jin daɗi nayi a zuciyata a fili kuma na ɗan basar cewa Hajiya Inna kenan waye ɗan iskan yaro kuma ? Dikko , Inna wai me yasa kikejin zafin Dikko da yawa ? Bana san yaron ne kwata² gaba ɗaya ya siremin kamar tusar safe....

      Saura kaɗan na fita na zageshi dan dai kar ace na haukace , ai bana nan ma dan ni bazanje ba , aiko sai kinje kodan ya ganki baki lalace ba ci gaba aka samu ba ci baya ba yaje ya bawa Dikko labari , nidai Inna gaskiya bazan wani je ba , aiko sai kinje kuma kin barbaɗa masa rashin mutunci yadda Dikko da uwarshi suka tozartaki kema sai kin tozartasu kuma sai ya baki sakinki tunda basu da mutunci....

    Inna kenan na faɗa a raina , a zahiri kuma na bita da kallo , kin wani tasani kina kallo kamar niɗin baƙuwarki ce ki wuce kije ki dawo , banyi magana ba na ɗauki hijabi na fice , a harabar gidan naga wata irin lutsetsiyar mota ɓaka sai sheƙin sabinta take tunda na taho nake ganin kaina a jikinta bana iya ganin na cikin motar shima a gilashin kaina nake gani saboda yana da duhu , jikina ya bani ba Dikko bane a ciki amma ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba duk inda wannan motar ta fito tashi ce kuma ban taɓa ganinta a cikin motocinshi ba ,

     A jikin motar na tsaya na ciki ya sauke gilashin motar tare da cewa sannu , yawwa na faɗa rai a ɗan haɗe , ya gida ? Lfy , kin gane ni ? Ey a Bakori daka kawo katifa a motar ka ko ? Murmushi yayi tare da cewa ashe baki da mantuwa , ya akayi ne ? Gefenshi ya kalla ya ɗauko wata "yar leda bansan ko miye a ciki ba ya miƙomin ba tare dana ansa ba nace meye a ciki ne ? Ki ansa koma miye zaki gani , hannuna ɗaya a ƙugu ɗayan nake nunashi amma bada ɗan yasa ba kawai ka faɗa danni bazan karɓa ba , ki ansa An mata , ban sake magana ba na juya na wuce dan kar in ɓata lokaci Inna ta biyoni ta yabamin , sallah na samu Inna tanayi nima abin sallah na shimfiɗa na kabbara sallah.

        Kai Ashiru ɗauki yaron nan ka maidashi gida fita zanyi , riƙe Dikko yaron yayi yana kuka cikin gwaranci yace bajan je ba tare da maƙale ƙafaɗarshi , Ashiru yace mai gida bazai zo ba , kai da Allah ɗaukarshi basai zaije ba ku tafi zanzo nima , ƙara riƙe Dikko Papi yayi yana kuka , kafin Dikko ya sake magana Abbakar ya shigo inda Dikko yake tsaye yayi parking tare da sauke glass yace DK bata ansa ba , ko tace maka wani abu ne ? Yadda sukayi da Sultana ya faɗa masa , babu damuwa An mata tana da matsala , ni bansa abinda ya faru ba tunda bana nan bazan iya ƙarda komai ba , kawai anje an kwaɓa abu duk sun jagwalgwale min komai , taya kai tsaye zan tunkari inda take bayan Momy taje ta ɗauko yaro ta taho dashi dole kowa zaiji babu daɗi , Momy Dady duk su ba'ayi musu dai² ba , itama Mamar kanta yayi zafi , kallon Ashiru yayi tare da cewa kiramin Umar yazo yanzu²n nan ya ƙarasa maganar yana kallon Papi daya duƙunƙune shi , isowarshi kenan su Nabeela suka zo dashi yi ma Dikko sannu da hanya da kuma dubashi da jiki , shi kuma sai wani bin Dikko yakeyi kamar yasanshi dan ko su Nabeela gajiya sukayi suka tafi suka barshi yaƙi binsu , iyakarshi gidanshi baije gidansu ba ,

KWARATA...Where stories live. Discover now