Page 30

5.8K 264 5
                                    

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_

                       *KWARATA*
      _{{Kalu bale gareku matan aure}}_

*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_

_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

                         &

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*

🅿 ------ 30

*_Ina miƙa saƙon ta'aziyya ga "yar uwar aikinmu Halima Yahya 20 Allah ya bada haƙurin rashi ubangiji yasa ta huta Allah ya kyautata namu ƙarshen idan ajaliyyarmu tazo...._*

     Amisty ta danneni da ƙarfin tsiya Hafsa ta sauka dan ɗauko igiyar da zasu ɗaureni da ita , murmushi nayi tare da kallon Amisty sannan na nunata da yatsa na juya na kalli Hafsa itama na nunata da yatsa sannan na gaggaɓe da wata irin dariyar dani kaina bansan na iyata ba ,

      Lokaci guda kuma na ɗaure fuska kamar bani nayi dariyar ba , da sauri Amisty ta kalli Hafsa suka kalloni a lokaci ɗaya , hawo saman gadon Hafsa tayi tana ƙoƙarin riƙe hannuna ta ɗaure , kallonta nayi kamar wata sakara sannan nace dake da Amina ku tabbata idan har kuka min wani abu kasheni shine kawai mafita a rayuwarku , amma na rantse da girman Allah wanda ya halicceni ya halicceku dani daku dukanmu shi muke bautama , mutuwa ta ko taku zata iya zuwa ko wane lokaci yanzu ko anjima , ko kuyi ko ku bari yanda kuka buɗemin sirri saina buɗe sirrin uban kowa a cikinki ,

      Bayan buɗewa saina tona musu asirin da ku kanku sai kunsha fiya² kun mutu saboda baƙin ciki , kar wacce ta ɗauremin hannu ko ƙafa kuyi duk iyakar iskanci da kuka iya , bashi ne kuma bazaiyi kyau ba a lokacin da zan biyashi akan iyayenku ,

     Muni , baƙin ciki , firgici , tashin hankali gaba ɗayanku zaku fuskance su yayin dana shigo rayuwarku , ina da illa kuma ina da bala'en haɗari haka nake dasa baƙin cikin da baya mantuwa a zuciyar duk wanda ya nemi ya dasa baƙin ciki a rayuwata , ciwo gareni haka nake da ɗaci kuka akemin kamar mutuwa yayin da na shigo gida dan ruguza farin ciki zuri'a ɗaya , ku lasa ku maida miyanku tunda kun buɗa ni kuma nayi alƙawari daga yanzu rayuwar farin ciki ta ƙare gareku ,

    Kallan kallo suka tsaya yi kowa da abinda take saƙawa a zuciyarta , tsoki nayi tare da cewa kuna ɓatamin lokaci domin ni ruwan ƙorama ce zuwa nake da ƙarfi na tafi idan kuma na tashi tafiya nakan tafi da abu mafi soyuwa ga al'ummar gari za'ayi ta tunani na har shekara ta zagayo ba'a gama wani kukan ba zan sake caɓar wani abun inyi gaba dashi haka mutane zasuyi ta kuka dani har ranar da mutuwarsu zata riskesu , dake da dake duk wanda na bari a cikinku ya huta ban yafewa kaina ba...

       Dukan ƙofa akayi da ƙarfi tare da cewa Hafsa me kukeyi kuma ? A shagwaɓa tace Mom ya akayi kuka dawo ne ? Ƙara dukan ƙofar tayi tare da cewa ni banje ba tunda na shigo nakeji ana ihu *kwarata* wai me ke faruwa ne ...?

      Dukansu shiru sukayi , ci gaba tayi da dukan ƙofar tana cewa wallahi idan kika bari na buɗe ƙofar nan da kaina zaki ci ubanki.... Cikin yanayin ɗacin rai Hafsa ta kalleni sannan ta sauka ta fara ƙoƙarin saka rigarta a lokacin har Mom inta ta zuro makulli ta waje ta fara buɗe ƙofa...

      Murmushi nayi da gefen bakina nima na sauka daga saman gadon na ɗauka towel in na ɗaura , ban gama ɗaurawa ba ta shigo ɗakin , kayana na ɗauka da makullin motar na raɓa ta gefenta zan fita , riƙoni tayi tare da cewa ke daga gidan ubanwa kika zo nan ke kuma....?

      Ko kallonta banyi ba da nace mata daga gidan ubanta nake , bakiji ina miki magana ? Kema nan dako haihuwarki ba'a gama ba har kin iya iskanci haka ? Kallonta nayi sannan na faɗa mata kaf abinda ya faru na ɗaura da cewa kuma na rantse da girman Allah saina rama ,

KWARATA...Where stories live. Discover now