ƘANWAR MAZA 8

1K 34 7
                                    

ƘANWAR MAZA
                

Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.
Ku yi following ɗina a arewabooks a kan account ɗina na ayshercool7724
Ko watpad Ayshercool7724 kowanne a cikin manhajojin za ku iya samun litattaiafaina da na yi a baya, da wanda nake yi a yanzu na gode

*Ina miƙa saƙon godiya, ga waɗanda suka yi mana ta'aziyya na rashin uba da 'yar uwa Naima Suleiman (Nimcyluv) ta yi, muna fatan Ubangiji Allah ya jiƙansa da rahama.*

*TAƘABBALALLAHU MINNA WA MINKUM, INA TAYA AL'UMMAR MUSULMI BARKA DA BABBAR SALLA, UBANGIJI ALLAH YA KARƁI IBADUNMU YA MAIMAITA MANA*


P8

Da rige-rige Usman da Abdallah suka shigo ɗakin, suna tambayar meyafaru da ruma take wannan uban ihun.
Kallonta Usman ya yi, ya kalli mama ya ce "Mama meya sameta ne?"

Mama ta ce "Ku tambayeta mana, ba gata nan a zaune ba"

Abdallah ya ce "Ke menene?"

Nuna masa hannunta ta yi, tana sake fashewa da wani uban kukan.

"Wannan ledar ta meye haka a hannunki, kamar wata miskiniya"

Ɓare baki tayi, ta cigaba da kuka iya ƙarfinta.

"Dalla ki rufewa mutane baki, kiyi mana bayanin menene?" Usman ya daka mata tsawa.

"Ba mama ce ba"

"Me maman tayi?"

"Ta yi mini lallen tsofaffi wai tsohuwa ta faɗa kwata ina bacci, wallahi dariya za ayi mini idan aka ganni da shi".

"Kuma saboda baki da mutunci, ki ke mana wannan uban ihun da Asubar nan, ke dai ba zaki yi hankali ba ko?"

"Wallahi mama ba ta sona, ban san meyasa ta tsaneni ba, wayyo Allah na"

Abdallah ya ce "Allah ya ƙara, a wannan shegen baccin naki, har aka yi miki lallen baki sani ba".

Mama ta ce "Ki tashi ki kwance lallen nan kiyi salla".

Ko motsi ruma ba ta yi ba balle ta tashi.

Abdallah ya ce "Wai wane irin lalle ne tsohuwa ta faɗa kwatar ne?"

Cikin kuka ruma ta ce "Irin fa wanda mama take yi a ƙafarta"

Dariya ce ta ƙwacewa Abdallah, ya ce "Haba mama, ya zaki yi mana haka?"

Mama ta ce "Hukunta ta nayi, duk rashin jin da take yi ba ta zaci ina da hanyar hukunta ta ba, na bada kuɗi ayi mata abin arziki na zamani, amma taƙi zama, ai da ni ki ke zancen, kuma ajima da kaina zan kai ki kitso zane huɗu za ayi miki".

Sosai ruma take kuka, Usman kuwa ficewa yayi ya cigaba da sabgarsa, Abdallah ne ya kaita bakin rariya, ya tayata ya cire ta wanke, aikuwa hannunnan yayi jawur, lalle ya kwanta ɗoɗar hannunta da ƙafarta.

Da gari yayi haske kuwa, Huzaifa ya ga lallen rumaisa, ya zauna ya sakata a gaba ya dinga yi mata dariya, har da kifawa, wai hannunta kamar kuturwa.

Ko Abincin safe ruma ba ta ci ba, sai kuka da goge hawaye, wajen ƙarfe goma na safe, mama ta sakata a gaba zuwa gidan kitso.

Kamar yadda mama ta faɗa, kitson hannu biyu aka yiwa ruma, gashi ta sha azaba a wurin mai kitson, saboda da ta ƙi tsayawa, mama na dukanta, matar kuma ta matse mata kai a tsakanin cinyoyinta, ga kitson azabar zafi tamkar za a zaro ƙwaƙwalwarta saboda yadda matar ke jan gashin.
Ko da aka gama kitson, ruma ta haɗa gumi ga hawaye da majina saboda azabar zafi, mama ta sakata a gaba suka tafi gida.

ƘANWAR MAZAWhere stories live. Discover now