ƘANWAR MAZA 18

801 36 2
                                    

                   ƘANWAR MAZA

Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES

P 18

*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHI YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR  DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA? TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN FATA NE? KO KUWA SO KI KE FATARKI TA DIN GA SHEƘI TA NA HASKAWA? MAZA KI GARZAYO WURIN MEENA DOMIN SAMUN MAFITA*

*Royal jelly big 22000*
*Royal jelly 30 pieces 2200*
*Royal jelly small one 60 pieces inside the pack 3000*
*Vitamin C-100, 2700*
*Vitamin E big 3000*
*Pesona 2300*
*Dara 2300*
*Cantik ayu 2300*
*GLUTA white 2700*
*Khusus ibu 3800*
*Sugar wanita 3500*
*Majakani 3 in 1 3200*
*Eve Care 3700*
*Juliet eve 11,500*
*Phyton buster 18,000*
*Phyton collegen 18,000*
*Glute sparkling 18,000*
*7 days ginger oil for hair 1,200*
*Papaya oil for breast 1,200*
*Garlic oil for hips 1200*
*Vitamin C serum 1,500*
*Vitamin E serum 1,500*
*Busty blend 2800*
*Gluta prime 2800*
*Collegen+C 3800*
*Yan uwa abun fa da yawa bazan iya kawosu gaba daya ba amma muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
*Wai ina da ku fans, ace haryanzu ban haɗa 1k subscribers a channel ɗina ba, anya akwai amana kuwa😒*

Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.

Sarai ya ji abin da ruma ta ce, amma ya share kawai ya tafi, dan idan ka biye mata babu abin da zai hana ta saka maka hawan jini.

Sai a lokacin ta samu zarafin dirarwa wainar da mama ta yi, ta fara ci ta na ajiyar zuciya, dan a kwanaki ukun nan Allah kaɗai ya san tsananin damuwar da ta shiga.

Yasir ya ce "Na so auren nan aka yi miki, mu ga ta tsiya, kowa ma ya huta da halinki"

"Ta Allah ba taka ba, bakinka ya sari ɗanyen kashi, na asuba mai tururi"

Mama ta ce "Meye haka, ki na cin abinci kina zancen ƙazanta"

"To mama ba sune suke tsokanata ba"

"Ina ruwanki da su, wato har kin samu kanki za ki ɗora daga in da ki ka tsaya ko?".

Ta girgiza kai ta ce "A'a, ai na shiryu ba zan ƙara ba"

"Kima cigaba, wallahi kin san idan ya zuciya da halinki, zai aikata abun  da ya ce"

Sallamar Abubakar da suka ji ne, ya sanya ruma yin wani zillo, ta daka tsalle ta yi waje, maƙalƙale shi tayi tana murmushi tana faɗin "Oyoyo yaya"

"Amarya ba kya laifi, kar dai har an ɗaura auren ban samu ɗaurin auren ba?"

Ta ɓata fuska ta ce "Yaya har da kai ko?"

"A'a, nima fa kirana aka yi a waya, aka ce mini yau ɗaurin aure"

Waiwaya ta yi, ta kalli mai sunan Baba da ya shimfiɗa tabarma ya baje litattafai yana dubawa, ta kalli Abubakar, ta kai bakinta kunnensa ta ce "Wallahi hussaininka ya ɗau hakkina, ba dan yayana bane ba ko? Hmmm"

Ya kalli mai sunan Baba ya yi murmushi ya ce "Kai, a wani dalilin ya sa ka ɗaga mana hankali haka fisabilillahi?" Ko ɗagowa bai yi ba, balle ya kallesu. Ruma ta kama hannunsa suka shiga ɗakin mama.

ƘANWAR MAZAWhere stories live. Discover now