page 11 to 15

716 32 0
                                    

💖 *INA ZAN GANSHI?*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

                11-15

Cikin takun ta mai daukan hankali ta karaso tafkek'en had'add'an office dinsa, office mai shegen kyau. s
Secretary dinsa Charles tayi kicibis ya fito rike da wasu doc a hannusa, da axama ya risina gaidata cikin harshen turanci.
Atakaice ta amsa.
"Mr Rasheed yana ciki ?
Yace "Baya ciki"
Bata jira cewarsa ba ta cusa kai cikin office din, binta yayi da duba ciki da mamaki halin rashin zuciya irin nata, ako yaushe saita baro department dinta taxo ganinsa amma ko kallo  bata ishe shiba, ba kuma shi zai hana gobe ta dawo ba.
    Lumshe idanu tayi ta karasakan swivel chair dinsa ta zauna shakar hadaddiyar kamshi dake tashi daga bisa kuma ta shingid'e barawo bacci yayi awon gaba da ita.

Agajiye likis yake driving harya karaso katafera building mai dauke da tambarin Mon, parking yayi, kafin ya fito guard uku sanye da black suit suka bude mai murfi hade da mika mai gaisuwa, ciki ciki ya amsa, ya fito hade da dagatar dasu ganin suna kokarin take mai baya, tsayawa cak sukayi ya wuce cikin building din, maaikatan  ciki sai gaida sa suke cike da girmamawa bai tanka ba banda haryan office dinsa ya nufa cike mamakin abu daya da yake a kullum idan yaxo office, idan kai ba komai bane ko kallo baka ishe mutane ba, laila kuwa yaro da kudi abokin tafiya.
Da azama charles ya mike hade da risina, "Good afternoon sir"
Hannu kadai ya d'aga mai bai tanka ba ya wuce cikin office, ranshi ne ya kuma bacci ya karasa kan daya daga cikin sofa dake gefe  ya zauna hade da daukar Wayar yana latsawa jifa jifa kuma yakan dago ya kalli yadda take baccinta anutse, yarinya kyakyawa tana bata lokacin sa akanta shifa bazai aure taba amma ta kasa ganewa. Koda yake laifin hajiya safara ce da take bata hope game dashi.

Charles ne ya shigo rike da wasu takaddau, ganinta yasashi ware idanu, sam ya manta Mardiyya ta shigo, idan bai tashe taba saidai kuwa ta kwana gurin yasan sarai Mr Rasheed baxai tashe taba, nufa yayi saitin ta yahau bubuga desk din, firgigit ta walka tana kokarin adjusting mayafin ta dake kokarin yarfowa kasa, kunya ce gabadaya ta kama ta ganin sa zaune saidai da alamun baisan tana gurin ba, mikewa tayi da azama ta gaida shi, bai tanka ba tayi saurin takawa bakin kofar xata fice taji yace karna kara ganin thin legs dinki agurin nan"
"toh" ta amsa cikin rawar ciki ta fice.
Kimtsa gurin charles yayi sannan ya ajiyemai takardun ya fice.

***
Salati tayi hade da mik'a bayan ta farka daga baccin wahalan da tayi, k'iran sallah magrib ya tabbatar mata da tafi awanni uku tana bacci, duk da tasan bacci sakaliya zuwa magrib ba kyau hakan bai hanata shingidewa ba, wani mugun yunwa taji ya turnuke ta sai sannan ta tuna da tun abincin African dish dataji da rana bata lashi komai ba.
Fitowa tayi daga dakin ta iske hassan da husaini na alwala gindin rijiya, sai yusuf dan karaminsu dake zauna yana cin shinkafa da wake. Hajjo sai kokarin kankamta gurin murhu take.
Mik'a ta kumayi akaro na biyu, tace "Hajjo kin gama abincin kuwa, har wani jiri jiri nakeji tsabar yunwa"
"Dayake ga uwarki baiwa ko, dan ubanki kizo kice tunda ke na girkawa, yar kusun uwa" Hajjo ta fadi cike da bacci rai, bata ko kalle taba tadau lankar samirar tayi cikin daki.
Dariya Hassana ya fece dashi, aranshi yaji dadi yadda Hajjo tayi mata, "toh ayi dai mu gani ko sabulu xai daina kumfa, "
Harara Batul takai mai tasan sarai inda ya dosa, tsaki tayi tace "banza kawai, toh munyi da toka ma yayi kumfa, kuma wlh ka shiga taitayinka idan bakaso nayi kudi na manta ka kasan dai ni matar manya ce"
Dariya yayi "wazai kwashe ki badai ..
Katse mai xancen Hajjo tayi daga daki, tana fadin "baza ku wuce masallaci ba ko ?
"Zamu" husaini ya fadi hade da jan Hassan suka wuce, dan shi dama magana ce makiyinsa, idan kaga yayi doguwar magana toh da Baba ne.
Cize baki Batula tayi danba karamin shak'a tayi ba, akalla shekaru shida ne tsakanin ta da hassan amma ya mugun raina ta, yaro dan shekara sha biyu sai ki rantse dan arba'in ne yadda yake tsaro xance. kallon yusuf tayi da har yanxu ya kasa cinye yar lomar dake cikin kwanon, tace "Kai tashi amso min salad da tumatur gurin Baba"
Kafin yayi magana Hajjo ta fito, bazai jeba, "ajiye abinci ka wuce sallah" ba shiri ya karashe loman yayi waje.  Ganin ba mafita yasa batul yin alwalar tayi sallah sannan ta zauna tsakar gida jiran ace ga nata abinci amma taji shuru.
Sallaman baba ne ya sata mike wa tsaye, ta amsa. "baba sannu da zuwa" ta fadi hade da amshe kwandon dake hannusa.
"Yauwa fatima, har kin dawo, ya makarantar ?
"Alhamdulilah"
Tabarma ta dauko ta shimfida ya zauna hade da shi mata albarka, itama zaman tayi tana kara mai sannu, baiyi mamakin abunda takeyii ba dan kuwa ta saba tarairayar sa, idan kuma halin nata ya motsa ko gaisuwa dakyar takeyi balle ta nuna su suka haifeta.
Fitowa da langar abincin Hajjo tayi, tamai sannu da zuwa sannan ta koma daki dauko furar dana dama mai, sannu baba" Batul ta kuma fadi akaro na biyar,
"Kinci abinci kuwa
Tace "a'a, dama kai nake jira Baba"
"Lailai kuwa kin cika yar baba, hada mata muci", ba shiri tahau zuba mai da yaji suka fara ci, Hajjo na fitowa tahau salati, dire furar tayi tahau Batul da dundun, "dan ubanki tashi nace, wannan abinci badake na dafaba, yar banxan yarinyar marar mutunci"
Murtuke wa batul tayi bata da alaman tashi,
Cikin sanyi muryarsa baba yace "waike Bareera ban hanaki zagin taba, baki san cewa wana bakin naki shine xai iya kaita ga halaka ba"
Hajjo kam ta kule "Malam ai dole nayi magana, yarinyan nan na ganina ina aiki ko sannu balle ta temakamin, nagama kuma dan batta kunya taxo ta baje tana ci".
"Ki dunga hakuri, Fatima ai yarinya ce komi tayi bai kamata ki hurar da ita da yunwa ba"
Toh" kawai hajjo tace ta koma daki ta zauna, tana jinsu suna hirar da dariya har sauran yaran suka shigo aka barke da hira.

***
Washe gari dakyar tasamu wata bakar doguwar riga ta sanya,yawanci yan atamfofin nata sun sha jiki, kunyar sasu take kar su Minal su raina ta, mayafi karamin ja ta dauko tayi rolling, fitowa tayi ta leka dakin Hajjjo ta iske tana sharar, tace "hajjo saina dawo"
Zuciyar hajjo fawas ta amsa mata da
Toh batula, Allah ya temaka, ki dawo dawuri dai"
"Amin" butula tace tana murmushi, shiyasa takeson Hajjo sam bata da riko kaman ba jiya ta kama d'addaurewa ba.

Zaure sukayi kicibis da Baba xai shigo ta gaidasa, yace da ita ta koma tasanya hijabi dan shigar ta tayau zam bata mai ba, ba musu ta sanyo hijab bayan ta saka mayafin cikim jaka, ta fito ta amshi kudin mota ta fice.
Bata sha wuyaba tasamu marwa ya kaita poly, da sauri ta wuce girl toilet ta cire hijab din tasaka mayafin sannan ta wuce zuwa hall, already su Minal sun kama mata sit, zama tayi tana wani shan kamshi ana gamawa suka fito da niyya wucewa gida kasancewar lec guda garesu.
Minal tace "Fatima yaushe zamu je gaida cousin dinki ?
Yatsine fuska tayi tace "very soon, baya gari ya raka mamansa Abuja checkup suna dawowa zamu je"
Allah ya kaimu" Minal ta fadi.
Billy tace "y not muje gidan ku"
Gaban ta ne ya fadi, aita gwamma ce su mata duka akan suje gidansu, mazewa tayi tace "okay muje, saidai Daddy baya gari yaje paris"
"Ba damuwa" acewar Billy.
motar Minal suka shige, billy abaya, Batul ta babbak'e agaba suka kama hanya, tunanin karya da zatayi kawai take, tafiya mai dan nisa sukayi har suka iso Kawo, billy tace" Minal shigar mu layin can na siyi salad da tumatur mai kyau"
"Ki bari akwai wani can gaba"
"Nidai muje can din, customer din mama ne, can take turamu siyo mata"
"Tonaji", lemcy tace hade dayin ribas, Batul jiki duk ya mutu,  Allah yaaa ba gurin Baba take nufiba, bata gama tsorata ba saida Billy ta nuna Baba dake nesa tana fadin karasa teburinsa....

INA ZAN GANSHI ?Where stories live. Discover now