page 63 to 68

556 28 1
                                    

💖 *INA ZAN GANSHI*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

              63 - 68

Cab ta gani pake gurin da azama ta fada tanai fadin mai unguwar da zai kaita, bai tsaya ciniki da ita ba, yaja motar, da isar su, fitowa tayi, cikin sheshek'a ta tambayesa nawa kudi, "oga ya biya" ya fada had'e dajan motar yayi gaba.
Mamaki da faduwar gaba ne suka diran mata.
"kodai Rmd yaga fitar tane" ta fadi a zuciyar ta.
   Kallon kofar gidan tayi tana tunanin makomarta, wani sabon kuka ne ya kufce mata dakyar ta iya samu courage din tura kofar langalangar ta k'usa kai ciki gidan hade da sallama.
     Zaune yake a tsakar gida bisa tabarma, kunnen sa nad'e da radio yana sauraro, jikinsa sanye da koriyar yadi da bakar hula bisa kansa, sauraran radio yake cikin nishadi da annashuwa.
Ciki ciki ya amsa, ba tare daya dago kansa dake kollan k'asa ba.
Arakub'e ta karaso gabansa hade da tsugunna wa, dukar dakai kasa tayi, kasa kallon sa tayi tsabar kunya shi dataji ya diran mata, ko adama ba wani k'are mai kallo take ba tsanin yadda take k'insa, yanxu data fara sonshi kunyar abunda tayi ya hanata ta dagowa.
K'ara sautin kukan tayi tace
"Sannu da zuwa"
Dago dakai yayi ya dube ta sannan yace
"Nina dace da miki sannu da zuwa, ya duniyar fatan dai kin samo abunda kikeso ko dayake amsa takardar ki ya dawo dake"
Kai ta girgiza hade da riko hannunsa.
"Mamuda dan Allah kayi hakuri ka yafemin"
Dan k'ara ya saki kadan tsabar azaban yadda ta matse mai tafin hannunsa.
Saurin sakin hannu tayi sakamakon jinin da taga yana diga, cike da kid'ima ta ciro hijab dinta tahau kulle gurin dake yanke. Bruises din jikinta ya kalla yana kara jin haushi kansa, hannu yakai gurin yana fadin "Batula miya same ki haka ?
Tsigarr jikinta ne ya tashi, ga wani uban radadi da gurin kemata.
"faduwa nayi" ta fadi cikin matsananci kuka, mikewa tayi da axama ta fada cikin dakinta, kuka sosai take tana tunanin yadda xata fadimai gaskia, saidai tsoro take karya rabu da ita.
    Jinjina kai yayi yasan zaa rina, shi kuma yadau alwashin idan bata fadi mai gaskia halin data shiga ba bazai cigaba da kasancewa tare da ita ba.
    Mikewa yayi hade da cire hijab din dake kulle hannusa ya fice daga gidan  zuwa pharmacy dan samun cikekken treatment.

Sallamar Almajiri ce ta katse mata kukan da take, hijab dake ghanarta ta ciro ta sanya sannan ta fito, mika mata ledar kayan miya da danyar shikafa yayi yana cewa maigidan ya aiko sa, amsa tayi sannan ta roki almajirin ya dibo mata ruwa a burtsatse, ba musu ya dauki bokitai dake gurin ya fice waje.
    Tun shigowarta bata lura da dakin Inna dake datse da k'wad'o ba sai yanxu da hankalinta yakai gurin, jiki mace ta nufi Bakin murhu aza wuta.

Har bayan sallah isha bai dawo ba, dan abinci data ajiye mai cikin samira tuni tayi sanyi, kara aza wuta tayi ta dumama sannan ta zauna bakin kofar dakinta jiran dawo warsa cikin tagumi.

Mikewa Mardiyya tayi dakyar ta karasa gaban drawer, janyowa tayi ta ciro magunguna kusan kala hudu sannan ta balle ko wanne tasha ta kora da ruwa dake rike hannuta a glass cup. Jiri sosai takeji, ta jima bata jita jikin yanayin ba, tsabar kuka da tayi ke barazanar janyo mata zazzabi, Shuru har dare bata ji motsin Saba atunaninta ko yana office, dakin Batul tuni ta duba bata cikin, kayanta data gani yasa tayi tsammanin ko ta shiga toilet gasa jiki dan tuni ta leka dakinsa babu kowa.
    Dakin Batul ta nufa, wayam ba labarinta, toilet ta leka babu ita balle alamun danshin ruwa, cike da tashin hankali ta nufi dakinsa nan ma ba alamun bil'adama ciki, tura kofar toilet tayi ta shuga, saidai jinin da broken mirror data gani yasata girgiza, azaman tsaftace gurin tayi cike da mamaki abunda ya faru, fatan ta daya kar ya zamana Rasheed ya jima princess ciwo agarin bugunta.
    Fitowa tayi ta leka office baya ciki, daki ta koma tadau wayarta tahau kiran sa no response.
    Saukowa kasa tayi ta nufi dakin Mom dake kwance kan gado tana kallon tashar Aljazeera a Tv, ganin Mardiyya ta fado dakin yasata daure fuska.
"Mom banga princess ba kuma Rasheed baya gida" akideme take maganar.
Tsaki Mom taja, tuni taga ficewa Batul da gudu ta window dakinta.
"Ta koma gidan Ubanta" ta fadi.
Ware idanu Mardiyya tayi tace "mom badai kin kore taba, kinsan dai Rasheed bazai ji dadi ba"
K'wafa Mom tayi
Tace "Mardiyya ki shiga taitayin ki, kinsa dai auran nan naki nice nayi insisting, Rasheed ba sonki yake ba".
Anzo gun, b'ata rai Mardiyya tayi, yau ita Mom kema gori, batace uffan ba ta juyawa zata bar dakin.
"Rasheed ba karamin yaro bane, he has the right to sleep duk inda yakeso dan bai dawo ba dat doesnt me ki hana kanki bacci" Mom ta fadi cikin kota kula da yanayin ta.
Karasa ficewa Mardiyya tayi cike da kunin rai, dakinta ta nufa ta kwanta cike da tunanin yadda rayuwarta zata kasance gaba.

INA ZAN GANSHI ?Место, где живут истории. Откройте их для себя