page 72

762 29 0
                                    

💖 *INA ZAN GANSHI*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

*IZG*

      *Kwadayin abin duniya* *Kwara ta wahala inta samu kudi shi won't know d value of it and she wil use dat to humiliate  d poor, gwara shi should be greatful to wat Allah destiny for ha, en she* *wil live happier without mach more money*
*Hankali kwance Aren't d poor one succeeding  en living peace ful in live* *without being wealthy enough?*

*Baga baban batul da maman ta ba da kannar taba,hankalinsu ba a kwance take ba? Basu ci ba su sha basu sutura?wake takura ma rayuwarsu?*

*Unlike Hajiya safara ,hajjo, RMD, Diyya duk ga harzikin amma ba kwanciyan hankali tareda su,kullun daga wannan sai wannan, Meh arzikin tayi masu?*
*Yasa ma masu kwanciyan hankali kodai tashin hankali  da hawan jini?*

*Hmmmm wani lokaci arziki ma wata bala'i ne wlhy Allah ya bamu wacce zata zama alkhairi gare mu da tsari kuma mai albarka*

                   💕 _*Ummiee Khaleel*_💕

*Nyc one Ummiee, after reading this intelligent write up i was like this girl really understand what am trying to initiate, it was so* *educative & remarkable.*
       *Thanks so much dear, i hope odas zasu fahimci* *sakon da muke son isarwa.*
   *All that Glitters is not Gold....*

                   72

Gabad'aya baya cikin hayyacinsa, jin ihu mardiyya akaro na biyu yasa shi dawo wa hayyacin sa, bakin kofa ya ganta Mom na kokarin turata waje.
"Sai kin bar gidan nan tunda bana ubanki bane" Mom ke fadi cikin daga murya.

Mikewa yayi ya karasa gurin.
"Mom plz calm down, xata bar gidan yanxu nan"
Kallon mardiyya yayi da har yanxu bata bar kuka ba, yace "bakiji abunda tace ba, wuce ki hada kayanki"
Kasa cewa uffan Mardiyya tayi saima kara sautin kuka da tayi ta bar gurin da azama, mara mata baya yayi ya fice daga dakin.
     Dogon Ajiyar zuciya Mom ta sauke ta koma gado ta zaune hade da dafe kanta tsabar takaici, Hajiya Safara idan kinsan wata baki san wata ba, nayi danasani gaya miki sirri na, saidai akwai certain things da baki sani ba.
    K'wafa tayi,  yazama dole tadau mataki akan Batul, dan bazata yadda danta ya kara auro bata, just jini daya da tace suke duk yabi ya rikici, she wonders ya zayi idan yagano ba kanwarsa ta jini bace, duk azuci take magana. Tunanin ranar data fara ganin Batul ta shiga yii...

Tuna Baya (Flashback)
Shekaru Shida da suka wuce.

Daidai round about ta kasuwar checheniya ta cikin jahar Kaduna ta hango sa daga can gefen titi suna loda kwandan kayan miyan cikin keken Napep, Gabanta na ya fadi, madubin fuskata dake nane bisa idanuwan ta cire cike da mamakin kara ganin sa, kusan shekaru ashirin da bakwai rabon ta da sashi a idanu sai yau tun bayan rubuwa da tayi dashi a katsina.
     Saidai ganin data mai ya tsofe ba kamar da ba, keken taga ya shiga matuk'in yaja su suka tafi.
   Saurin tada motar ta tayi zuciyar ta na azalzalarta ta bishi taga ina zai nufa, can cikin unguwar kawo taga keke ya nufa, tsayawa yayi daidai wani gidan bulo da babu sementi, daga cen nesa tayi parking tana kyallarosa.
     Kyakyawan Yarinyar yar kimanin shekaru sha biyu taga ta fito gidan, jikin sanye da kayan makaranta na islamiya, gaida sa tayi ya fiddo naira ashirin ya bata sannan ta wuce, sai kuma maza biyu masu kama taga sun fito, suma sanye da kayan makarantar, gaidasa sukayi suka wuce.

Duk akan idonta, karaso wa Satin Motar ta yarinyar tayi natai karewa motar kallo, baa ganin wanda ke ciki kasancewar ta tinted, nan Mom ta samu daman kare mata kallo sakamakon hannu datasa tana taba motar cike da sha'awar ta,
"Batula munyi latti fah" Hassan ya fadi yana juyowa baya dan tuni sun yi gaba"
Guntun tsaki taja tace "oh ni fatima, yaron nan bazai daina kirana batula ba" ruguwa tayi tanai ihu su jirata.
Maida dubanta Mom tayi zuwa gurinsa saidai tuni ya shige gida, mai keken ma baya gurin, dogon tsaki taja hade da buga steering, taso ace ta samu details akanshi, reverse tayi kokarin yi taga wani dattijo ya shiga gidan ya fito cikin sakanni kalilan rike da kwandan albasa, ganinsa tayi ya karasa wani teburi hade da ajiye albasan akai
   Saurin jan motar tayi garesa, sannan tayi wining glass.
"Sannu" ta fadi
Washe baki abokin Baba mai suna Lamido yayi, tambayarsa tayi nawa kwando albarsa, yace da ita dubu da dariya biyar, dubu biyu ta fiddo tabasa hade da barmai cancin, godiya sosai yayi.
Tace "naga wani da kayan miya ya shiga can gidan, waye shi ?
Dariya lamido yayi "muhammadu ne shine mai teburin ai, nazo ne kafin ya karaso"
Murmushi dabai kai zuci ba Mom tayi tace, "ayyo, naga yaran sun fito daga gidan yanxu, halan yayan sane"
Lamido yace "su yan biyu ba, hassan da hussaini yaran sane"
K'wafa Mom tayi, aranta tana fadin wato shi aure yayi ita tana can igiyoyin akanta, afili tace "naga wata yarinya tare dasu, wace ita.
"Yar'sa ce ta fari"
Gabanta ne ya fadi.
Yacigaba "bayan mutuwar danuwan sa ya auri uwar yarinyar wato ikilima, kinga kuwa shine ubanta kuma amatsayin yarsa ta fari".
Bata cira cewar saba taja motar afusace tabar gurin, wani mugun tsanar sa da yaran taji azuciyar ta, ba mamaki Ikilima matar kaninsa Ahmadu ya aura, sunyi zaman gida daya dasu a kauyan kafin hausa, kuma zaman baiyi dadi ba, dan alokacin basa shiri da Ahmadu ko kadan dan baya daukan raini daga baya ne ma tafara girmama shi Amma toh yaushe rasu, ta tambayi kanta... Rai bace ta koma gida ba tare data fadiwo kowa xancen ba.

INA ZAN GANSHI ?Where stories live. Discover now