page 71

590 31 0
                                    

💖 *INA ZAN GANSHI*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

*Special greetings to IZG* *fans, thanks much for the* *love & Support, ILYSM*❤                 
*TeamDiyyah*❤

                  71

Daskarewa Rasheed yayi, tashin hankali da firgici shimfid'e bisa fuskar sa.
   Shi kansa Alhaji Bello ware idanu yayi yana sauraran karin bayani, kallan wulakanci tamai sannan tace
"Alhaji ka fita idanu na, kaga adalilin nacin ka na furta abunda ba hakan bane, tunda kaki ganewa gwada nama b'aro b'aro, bana sonka dan Allah ka shafamin lapia".
Hular kansa yahau gyarawa yana fadin "Allah ya baki hakuri, kinga tafiya ta" ficewa yayi daga palon batare daya jira cewarta ba.
     Ajiyar zuciya ta sauke ta maida dubanta ga Rasheed da itama kallonta yake
"My boy dont mind my words, haushi yaban yasa na furta hakan, babu wani aure akaina"
Cikin rashin gamsuwa da maganar yace "kince my Dad is alive"
Kwantar da Murya tayi tace "bakaji nace kawai fada nayi ba, believe me your Dad is dead".
Baice uffan ba ya fice parlour ba tare daya gamsu da abunda tace ba. Tunda har ta furtan hakan akwai kamshin gaskia ciki, idan ma koran Abba mardiyya take sonyi ai akwai oda strategies da zatayi using ba wannan ba.
      Main palon ya k'arasa ya zauna yana tunanin wazai tuntuba da batun yadda mutuwar Babansa ta kasance, kawu Habibu ne ya fadomai arai, tabbas shi d'aya zai iya fayyace mai ko Babansa nada rai koya mutu, duk azuci yake xancan, dafe kai yayi, gabadaya duniyar tamai zafi, bai gama nutsuwa da b'atan Batul ba ga wata gagaruma Mom ta janyo mai.
     Mikewa yayi da zama ya haura sama zuwa dakinsa. Freshen up ya shiga toilet yayi ya fito, ya shirya cikin kananun kaya, ya sauko kasa ya fice haraban gidan, motarsa yafada yaja zuwa home of hospitality (katsina).
     Cikin sa'a ya iske kawu habibu gida bai fita ba, gaisawa sosai sukayi daganan ya zayyano mai xancen dayaji Mom ta fada.
Jinjina kai kawu Habibu yayi yace.
"Tabbas abunda ta fadi ta fade sane kawai dan wata manufarta, amma kam Baban ka ya dade da rasuwa, tunshi kuma bata sake aure ba"
D'aurewa kan Rasheed yayi da kalaman kawu, yakasa aminta da abunda suke fadi, shidai yasan akwai wata boyayyen al"amari dan jikinsa na fadi mai babansa na raye tunda Mom ta furta.
Nisawa yayi yace "kawu miye sanadin  mutuwar sa, kunyi mai jana'iza ?
Girgiza kai yayi, yace
"Bana nan sanda ya rasu, ina Ghana karatu lokacin, bayan na dawo Maman ka kece min ya jima da rasuwa, nayi kuka rashin sa ba kadan ba, tsohonka akwai halin kirki da daddako"
"Allah yaji kanshi" Rasheed ya fadi asanyaye, saidai ayyada ya lura da xancen Kawu bai da matsaniya akan mutuwar Baba, same story da Mom tabasa shine wanda yasani, ba yadda ya iya dole ya nunawa kawu ya yadda da xancensa dan bazai iya mai masu ba.
Sun dade suna hira daga bisani yamai sallama ya kamo hanyar dawo wa Kaduna.

                *Zaria*

8.26pm

Iya karfinta ta sanya tana wanke shinkafa wainar gobe, daga can gefe Inna ke zaune tana yankar alaiyaho.
"Ilimi akwai dadi, Inna nima dai xan shiga islamiyyar daran nan" Batul ta fada tana sauraran karatu dalibai dake tashin daga can islamiyar dake gaba dasu.
Inna tace "Islamiyar akwai karantarwa, babu wasa sam, yaro kadai xan tura ya karbo maki form ki ciki gobe ki fara zuwa'
Cikin jin dadi tace "nagode sosai Inna".
Yaro ya shigo hade da sallama, amsawa sukayi yace "Nafi'u mai shayi ke sallama da jikar mai waina, yana waje"
"Kai yaro koma kace bata fitowa" Inna ta fadi tanai zarowa yaro ido, tasan xaa rina sunga yar kyakyawa zasu fara damunta da k'wado sallama.
Dakatar da Yaro Batul tayi tace "kace mai gani nan"
Toh" yaro ya amsa ya fice.
Kallon Inna tayi tashe, "inna kiyi hakuri naje, kinsan shi  dan adam komin yadda yake ba abun wulakantawa bane, wannan abu ya faru akaina, banaso tarihi ya kuma maimaita kansa.
Dariya Inna tayi, tace "gaskia ne, kije amma karki dade".
Hijabin ta dake lankaye kan igiyar shanya tadau tasa ta fice wajan gidan.
      Tsaye ta iske shi, hannusa rike da bakar leda, jkinsa sanye da kodaddiyar tshirt da wando daga ganin wankan kure adaka yayi.
"Ina wuni" ta fadi hade da sunne kai kasa, tasan dama saiya biyota, dazu dataje teburansa siyan biredi sai wani kirki yake mata.
"Lapia kalau yammata" ya amsa.
"Sunana fatima" tace
Yace kiyi hakuri nakira ki da yammata, gaki da babban suna"
Murmushi tayi tace "ba komai, ya kasuwa ?
"Alhamdulilah" ya amsa mata.
Shuru ne ya biyo baya, sai can kuma yace "fatima tunda naganki naji sonki araina, dan Allah ki bani dama na nuna maki tawa salon soyyayar.
Murmushin dayafi kuka ciwo tayi, tuni ta cire so aranta, shi kuma gashi yaxo da kokan baransa, dago dakai tayi ta dubesa, Nafiu ba laifii dukda ba sonshi take ba tana iya aurensa, yana da kirki hankalinta zaifi kwanciya dashi.
Nisawa tayi tace "nagode sosai da Soyayyar ka, Allah yasa hakan yafi alheri".
Dadi sosai yaji ya mika mata ledar hannusa, kin amsa tayi, yace "ki karba, biredi ce na taho maki dashi"
"A'a wlh ka barshi, so kake na cinye ma jarinka"
Dariya yayi, ba yadda baiba ta karba taki amsa, hira kadan suka dan tab'a, tamai sallama ta koma gida, tuni Inna ta shige daki, zama tayi tsakar gidan tanai tunanin Baba da hajjon ta, kiransu take sonyi saidai wayar ma batasan a wace duniya ta yarba tsabar rawan jikin zuwa nema Rmd, ba mamaki ranar datai gudun nan Inna ta biyota wayar tafadi daga hannuta.

INA ZAN GANSHI ?Kde žijí příběhy. Začni objevovat