page 74

769 29 0
                                    

💖 *INA ZAN GANSHI*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com


                 

                  74

Kuka take sosai cikin tsananin tashin hankalin da bata tab'a fuskanta arayuwarta ba. Turo kofar dakin yayi yana fadin, "Princess baza ki fito breakfast.." Makale wa kalaman sa sukayi a mak'o shinsa ba tare daya ida ba sakamakon ganin dayay mata.
    Sauri goge hawayan fuskanta ta hau yi amma tuni yagani, kasa daurewa tayi da boye damuwar ta karasawa gabansa tayi hade da fadawa jikinsa tanai kuka mai tsuma zuciya.
Cike da tashin hankali ya rike to suka zauna kan gadon,
"Princess mike damunki, waya tab'amin ke" ya fada yanai kokari dago da fuskarta dake boye cikin kirjinsa.
Kuka take tana tuna kashedin da Mom tayi mata, mudin idan tafadi ma Rasheed bazata barta lafiya ba, saurin tsayar da kuka tayi, ahankali ta dago da fuskarta suna fuskantar juna.
Baki na rawa tace "tsoro nake ji"
"Tsoron miye ? Ya fada yana kawar da gashin kanta dake neman tsone mata idanu.
Sabon kuka ta fashe dashi tana fadin,
"Mutanan nan su nake gani a mafarki zasu kamani"
Hannu yakai bayanta yana lallashin ta "Plz dont cry, its just a dream, babu wanda zai kamaki"
Kai kawai ta daga mai, lalashin ta sosai yahau yi saida yaga tabar kuka sannan ya lallabata ta shiga wanka, Parlour ya koma ya cigaba da cin breakfast dinsa akan dinning, tuni Mardiyya ta kammala cin nata abinci, zaune take kan kujerar apalo tana kallon Tv.
    Cikin bakar abaya Batul ta fito, bata karasa Dinning ba ta zauna kan kujera hade da gaida Mardiyya.
"princess baza ki ci abinci ba" Mardiyya ta fadi ganin bata da niyya tashi.
Yaken dole Batul tayi, aranta tana fadin ashe da ex kishiyata nake zaune ban sani ba, afili tace "zanci, xuwa anjima"
Kafin mardiyya takai ga bata amsa ya mike daga ina yake zaune yana fadin "Diyyah dauko min abincin ta" karaso yayi ya zauna kusa da Batul.
Abincin Mardiyya ta dauko a plate ta mikemai hade da mango juice cikin glass cup.
"Tnx dear" ya fadi hade da amsa.
     Kallon Batul yayi da tuni tafara yamutse fuska, diba yayi a spoon akai bakinta, dauke kai tayi alamun bazata ciba.
"Zan dauko Bulala fah "ya fadi hade da daure fuska.
Tsoron duka taji, ba shiri ta jiyo yanai feeding dinta tanai zuba mai shagwaba, dakyar tasamu ta iya cin rabi tace ta koshi, juice din yabata tasha sanna ta langwab'o jikinsa.
"Prince yaushe zamu je zaria" ta fadi kaman zatai kuka.
Cheeks dinta yadan ja cikin salon wasa yace "kin fiya son yawo, gobe if am less bizy sai muje"
Kare shigewa jikinsa tayi hade dayin Lamo batare data ce uffan ba, runtse idanu tayi tana sak'a da warwaran yadda zatai convincing dinsa.
      Shuru dayaji yasa ya dubi Mardiyya da gabadaya hankalinta na kan Tv, yace "Diyya dauko min Car key dina adaki"
Ba musu ta mike ta shiga dakin ta dauko.
Mikewa yayi ahankali hade da kwantar da Batul kan kujerar, amsa key din yayi yace da ita ya tafi office sannan ya fice.
   Plate dake gurin ta dauka ta nufi Kitchen ajiyewa, mikewa zaune Batul tayi hade da dafe kanta, duniyar gaban daya tai mata zafi ji take tamkar ta shige karkarshi kasa, jiki sanyaye ta mike tsaye ta fada dakinsa, wani irin sanyayyar kamshi da sanyi ne suka bigi hancinta, kwanciya tayi kan gadon cike da tausayin kanta.
     Fitowa Mardiyya tayi daga kitchen ganin Batul bata palon yasa tayi tunanin ko ta shiga dakinta, zuciya daya ta shiga dakinsa da niyya kwanciya ganin Batul kwance kan gado yasa tayi azama juyowa ba tare data karasa shiga ba, Dakinta ta nufa ta zauna kan gado hade da daukar wayarta, dialing nambar Hajiya Safara tayi, ringing daya, biyu ta dauka daga can bangaran.
"Hello, Umma ina Kwana" ta fadi cikin yanayin ba yabo ba fallasa.
"Lafiya lau Mardy, ya kuke, fatan dai shegia matar nan bata tsangwame kiba ? Acewar Hajiya Safara
Takaici ne ya kama Mardiyya tace "plz Umma ki bar fadin haka, kinsan dai maman mijina ce kuma she deserve some respect"
Tsaki Hajiya safara taja.
"Toh uwar son Miji, sai kiyi ai, ya jikin naki ?
"Da sauki, nasha magani"
"Idan kin shirya zuwa Asbiti kimin magana sai muje" acewar Umma.
"Toh Umma" Mardiyya ta fadi, hira kadan suka dan tab'a sannan ta katse.
     Ajiyar zuciya ta sauke tana xancen zuci, "am sorry Umma, wannan karan na sab'a maganar ki, kusan shekara daya ina zuwa asibiti ba tare da saninki" tunani tahau yi hawaye na d'isa bisa fuskarta.

INA ZAN GANSHI ?Onde histórias criam vida. Descubra agora