page 21 to 25

647 31 0
                                    

💖 *INA ZAN GANSHI*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

             21 - 25

Daidai inda rumfar Baba ya tsaya duk suka sauko yahau agazamai sauk'e kwandon. Batul kuwa bata jira komai ba tayi gaba da azama.
"ke yazaki gudu baki bani kudi ba ? Mamuda ya fadi ayayinda yake kokarin dire kwando hannunsa, bata juyowa ba balle ta tanka banda saurin da takeyi, nisawa Baba yayi yace "ya'ta ce, zan biya gabadaya"
Sunne kai yayi, kunya Baba yaji ya lulub'esa, inda ya biyemata yaukam da girma ya fad'i, taimakon Baba yayi  da wanke tumatir sannan ya tayasa kaso, albarka sosai baba ya shimai, dukda ba wata doguwar hira sukayi ba amma tsohon ya kwanta mai arai, yana shirin tafiya Husaini ya k'araso gurin ya gaida sa aladabce, ciro dari takwas Baba yayi ya mikamai, fir yaki karba, ba yadda baba baiyi ba, ganin yaki karban halal dinsa yasa baba yace Husaini ya kaisa gida yaci abinci kanan ya wuce, dukda Mamuda baiso hakan ba amma wata xuciyar ta tursasa mai son xuwa gidan.
    Hassan tsaye gindin rijiyawa yana wanki, sai yusuf dake zaune daga gefe yana homework, Hajjo ta fita mak'ota barkan haihuwa,  Sallama sukayi Hassan ya amsa suka karaso ciki ya gaida shi, "Batula fito ki sawa bak'on Baba abinci" Husaini ya fada daidai tsetin dakin, kayan jikinta take ragewa tasanya wani kod'adda tshirt da zani, tana jinsa tayi banza banda kokarin bude ostrich ledan ta da take, sake maimatawa yayi sannan ta amsa mai, "Batula yafita daga bakinka kafin na fito na wanke ka da mari"
"Tofah, Manya na magana" Hassan ya fada yana dariya, harara Husaini yakaima,  ya kalli Mamuda yace kayi hakuri bara na zubo ma" tabarma ya shimfada mai sanan ya zubomai dambun hatsi da Hajjo tayi, murmushi Mamuda yayi hade damai godiya yahau cin abinci da tunda uwarsa ta haifesa bai taba gamo dashi ba, haka dai ya daure yana cusawa.

Fitowa tayi daga dakin rike da ledar tana shewa, batama lura dashi ba tadau kujerar tsugunno ta zauna tsakaiyar gidan, "yehoo ku fito yau party zamu.." Ido hudu sukayi ta kasa ida maganar, sai kuma ta dauke kai kaman bata sanshi ba gudun kar yayi mata magana su Hassan su dauka ko saurayinta na.
"Party nami" Hassan ya tambaya.
Ta gefe ido ta kalli Mamuda sanna tace "kayan dadi sabon saurayi na ya tsiya min, idan kunaso na baku zakamin wanki, shi kuma husaini yamin guga, auta kuma ya gogemin takalmi" ta karashe maganar tana kallo yusuf da tuni yawu ya tsinke mai, atake Hassan ya yadda ta mika mai burger ya karba yana santi, yusuf kuma ice cream aka bashi banda husaini daya hada rai bayaso.
Hassan yace "wai waye saurayin nan naki, yana zuwa nan ?
Fari tayi da ido, "mai kudi ne ba lailai ne kasan shiba, kana jin labari wani Rmd, most influential family a garin nan"
Yace "gaskia bansan shiba, halan shi ne saurayin naki ?
"Eh fah shine, very soon xai turo gaiswa".
Wage baki Hassan yayi yana kallonta, yasanta sarai da karya amma wanan kam ya wuce tunaninsa, kwashewa yayi da dariya yace " uwaka karya, ubanka karya, Batula kinayi ina jin dadi kina bari ina jin haushi, ina mai kudi ina talaka irinki, dan Allah ki rage ta gobe"
Kowa gurin saida ya kwashe da dariyar abunda Hassan yace, Mamuda kam harda rike ciki yana darawa, yarinya ga kyau amma ba kyau halin, saidai yadda take karya in a classy way ke kara bashi dariya.
Akule ta mike tsaye, "banxaye sai kuyi tayi dai, yan bakin ciki" fuu ta wuce daki da kunin rai, tana jiyosu suna kara darawa.
Mikewa mamuda yayi yamasu sallama ya fice dan kuwa idan ya xauna yana iya amayo kayan cikinsa, gurin baba ya nufa yamai godiya samlnna ya wuce.

****
A firgice ta farka tana karewa dankareran palon kallo, hamdala tayi da Allah yasa mafarki tayi ba dagaske bane da yau hankalin ta tashi xaiyi idan 
My boy ya gano akwai boyayyan al'amari da take boye mai sama da shekaru talatin. Altine ta kwalla wa kira ta kawo mata fresh milk tasha ta shingide cikin kujerar tana kokarin kawar da rayuwar past dinta dake neman dawo mata sabon fill ababin rayuwarta na yanxu.
Sallama sa ce ta katse mata tunani, ta amsa cikin boye damuwar ta, karaso wa yayi kusa gareta, "Mom are you alright, naga your face is pale"
Murmushin dabai kai zuci ba ta sakar mai, "am, good, ya yau din ?
"Lapia kalau, i really enjoy it" ya fadi yana murmushi, itama murmusawa tayi cike dajin dadin ganinsa cikin farin ciki, bisa cinyarta ya ajiye kansa tasa hannu tana kwantar mai da lausasan gashin kansa, tace "Abdulrasheed yau kasani farin ciki, alway b happy kaji?
"I'll Mom" ya fadi yana kara fadada fara'arshi. Wayarsa ya laluba aljihu ya ciro yayi daillng no din Mardiyya, zaune take tsakiyar gadonta Tana tofa addu'ar bacci taga call dinsa, tsoro da mamakine ya kamata by diz tym ace ya kirata, jiki sanyaye ta dauka, tayi shuru.
Murya kasa kasa
Yace "Mardiyya hope dai ban tashe kiba ?
Dadi taji yadda ya kwantar da murya tace, "banyi bacci ba, ya daran ?
"Cool'
Shuru tayi tana juyo heart beat dinsa, nisawa yayi yace "mi kika dauka a office dina ?
Gabanta ne ya fadi itakam bata dau komai ba banda daya daga cikim hanky dinsa data zara amma kuma bata san inda ta ajiye ba, tace "ban dauki komai ba"
"Are you sure ?
Tsoron Allah ne ya shigeta, karya itace abunda bata iyaba, "am sorry Mr rasheed   na dauki hanky dinka without ur consent"
Ajiya zuciya ya sauke, "ina hanky din yake"
Cikin rawar murya kaman zatayi kuka tace "i lost it"
Abinda yake sonji kenan, katse call din yayi, aransa yana tunatin where on earth ita kuma wacan tasamu hanky dinsa, Mom ce ta katse mai tunani da cewa "my boy nasan kana santa, ka aureta i promise you won't regret it"
Kallon rashin fahimta ya daga kai yay mata, tace "dont be silly, who else idan ba Mardiyya ba"
Yake kawai yayi ya maida kansa, zuciyar na bijiromai abubuwa da dama.

****
Yau da wuri taje lec ta dawo kasancewar ruwa da akayi ta makawa yasanya yawanci lecturers basu zoba, tana ganinsa tare da Baba akaramin zauren gidan ta bata fuska, shishigin yafara isarta tun ranar daya sauke su akullum sai yaje teburin Baba hira, yanxu kam tamkar yaron baba haka ya zama duk wani aike da dauko kayan miya gurin tsari shi Baba ke aika, takai ma yanxu sun saba da Hajjo, har wani kwanan abincin daban take ajiye mai.
Baba sannu" ta fadi cikin hade rai, dama akulle ta dawo da haushi Billy yau data tsitsaye ta akan deceiving dinsu take, fada sosai sukayi saida Minal tasa bakin akan lailai gobe saita kaisu gidan su cousin dinta Rmd, karfin hali kawai tayi ta amsa masu da naam, ranta duk ajagule ta rasa mafita.

Kallon ta Baba yayi, yanayinta ya nuna ba lapia ba, yace "fatima mike damunki ?
Kuka ta fashe dashi "Baba nikam na gaji da talaunci nan, wai yaushe zakayi kudine, miyasa ma na fado cikin zuria ka" sosai tafashe da mugun kuka, kollanta Baba kadai yayi yana murmushi bayau mace tasaba cin zarafin saba, saidai kalaman fatima ba karamin fama mai ciwo daya dade da samun waraka azuciyar saba.
Ran mamuda kam ya gama bacci hannu ya daga da niyyan sharara mata mari, baba yarike hannusa "dukan mace bai kamace kama, karka kuskura" Acewar Baba.
Harara Batul ta kaimai ta ruga gida aguje, baba ya rike hannusa suka fice zuciyarsa na tafarfasa.

Gam Hajjo ta capke ta data shigo, dan kuwa duk abunda tace taji ta, kaman an aikota tahau Batul da dukam tsiya, banda ihu da kuka ba abunda take,
"Kafin ki kashe ubanki ni xam kashe ki" hajjo ke fadi cikin kunin rai tana mai kara kai mata naushi, saida tayi mata lillis sanan ta barta tana fadin "yar banxa yarinya, kasheki xanyi na huta da bakin cikin ki, nagode wa Allah daya azurtani da kannanki dayau kin kasheni abanza"
Kuka sosai Batul take, tana jawa bawan Allah mamuda Allah ya isa, aganinta tunda yaxo hajjo ke kirbanta, dan kuwa rannan abinci taki zubamai hajjo ta mata lilis yauma ba, wani mugun tsanan shi take ji aranta, ayyada zuciyarta ke tafasa inda zataga Rmd binshi kawai zatayi tabar masu gidan, dan kuwa shine kadai gatan ta yanxu.
"Oh ni fatima ina Xan Ganshi,.." Ta karasa magana cikin matsananci kuka, atunanin ta a zuciya ta fadi not knowing afili tafada, jim muryar Hajjo tayi akanta rike da ludayin miya, tana cewa , idan na fasa maki baki zaki ganshi da kyau"
Ba shiri ta mike da azama tayi cikin bayi da gudu tana kuka.

INA ZAN GANSHI ?Dove le storie prendono vita. Scoprilo ora