page 73

710 31 0
                                    

*INA ZAN GANSHI*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

                   73

Shuru babu alamunta, har dalibai suka k'arasa fitowa, Mai gadin gurin ne ya mike hade da kokarin kullo gate din.
Yace "dan dakata, karka kulle kanwata bata fito ba"
Karasa kulle gate din yayi hade da datseta ta k'wado, sannan ya kallesa yace.
"Lokacin rufewa yayi, saidai ka duba karamar kofar baya"
Nagode" yace da dashi yayi azaman zagawa baya.
Dalle mata idanu Roze yayi yana kallon fuskarta, kallon hoton wayarsa yayi yace da sauran ita dince, ku dauke ta kusa ta cikin mota.
Tsoro ne ya dabaibayeta, kallon su take bata gane ko wanne cikin su ba sakamakon mask dake sanye fuskar su, kuka ne ya kufce mata tahau rokonsu, ko sauraranta basu yi ba sukayo kanta, ihu ta kwalla, dabarar tsugunnawa tayi ta kwaso kasa ta watsa masu fuskar. A 360 ta arta aguje, cikin tsananin fusata suka bita da gudu suna goge idanuwa da shikadai ke bayyane cikin mask din.
      Ihun ta daya karad'e dodon kunnansa yasanya shi saurin barin gurin da tuni ya iso yana jiran ganinta, cike da tashin hankali yahau zubawa hanyar ido, daga nesa ya gano katti na gudun famfalaki, motarsa ya fada da azama ya fuzgeta afusace.
Gudu sosai take. Tsabar kid'ima wuce layin gidan Inna tayi ta fada makarantar UBE dake fuskan tar ta, ajin farko ta fada ta karasa can karshe ta boye karkashin desk, dagowa tayi ahankali tana lek'e ta window, tsaye tagansu daka can nisa suna leka ajujuwan dake gefe, aji biyu kadai ke tsakani kafin su karaso inda take. Sosai hankalinta ya tashi tanai sharar kwalla, ziro kofofinta tayi ahankali ta window ta fito kasancewar babu glass, tuntube taci da dutsen dake gurin ta kwalla ihun daya janyo attention dinsu gurun, da axama suka fada ajin tare da baza idanuwa.
     Cike da radadi da azaba ta falla da gudu, bata ankara ba taji hannu ya rikota, ihu xatayi yayi saurin sa hannu ya toshe mata baki, janta yayi suka lafe cikin bishiryar dake gurin, runtse idanu tayi tuni ta sadakar sun kamata, saidai kamshi prince dinta dake bugar mata hanci yasata faduwar gaba.
Hannu yakai bisa fuskar ta yanai share mata kwalla, cikin sanyin muryar sa ya kira sunanta da princess, kin bude danu tayi banda rawa da jikinta yake, atunanin ta bashi bane, zuciyar ta keson yaudarar ta.
"Princess baxaki bude ido ki kalli prince dinki ba"
Bude idon tayi ahankali ta daura sa bisa fuskarsa, kuka ta fashe dashi ta fada jikinsa tana fadin "i know you hate me but plz ka temakeni kar mutanan nan su kamani, plz save me" kuka sosai take tana maganar.
Baice komai ba, yasan inda xancen ta ya dosa, rikota yayi suka karasa motarsa yabude yasanya ta ciki sannan ya shiga yaja.
    "Oh shit" Roze ya fadi adaidai lokacin da suka karaso yaja motar, kallan yaran yayi yace operation continues tomorrow, jiki sanyaye da haushi rashin kamata suka bar gurin.
     Kuka kadai take a motar har suka karasa gidan Inna, kafin ya daidaita parking tuni ta sauko ta ruga cikin gidan, daki ta nufa hade da rufo dakin ta ciki.
      Mikewa Inna tayi daga inda take zaune a tsakar gidan.
"batula lapia kuwa" Inna ta fadi cike da tashin hankali, ganin rasheed ya fado adan kidime yasa ta kallesa tanai tambayar sa make faruwa, bai iya amsa taba ya karasa bakin kofar yanai bugama Batul kofa hade magiyan ta bude. Banxa tayi dashi tanai cigaba da kukanta.
      Yaro ne ya shigo yace Nafiu mai shayi na sallama da Batula, daga Shi har Inna kasa tanka yaron sukai, Batul dake jinsa ta bude kofar ta fito, bata ko kallesa ba ta raba gefensa tayi waje, Sauri binta yayi ya tsaya bakin kofar ganin ta tsaye gefe kusa da wani saurayi.
    Gaidasa tayi cikin kokari boye yanayinta, cike da farin ciki ya amsa, yahau ta da hira da ba fahimta take ba, banda eh da a'a dakadai take cemai, gabadaya hankalinta baya tattare da ita
Yace "fatima yaushe zamu je ki gaisa da iyayena, na jima ina basu labarin ki"
Yaken daya fi kuka ciwo tayi tace "duk randa ka shirya sai muje"
Dariya yayi.
"Toh amarya yata, Allah ya kaimu, nizan wuce sai da safe.
"Haba dai, tun yanxu" ta fadi ita kanta ta kosa da hirar, saidai ganin Rasheed tsaye gurin yasa batason ya tafi.
Tsayar da Nafiu tayi na kusan awa daya sannan sukayi sallama ta shigo gida.
     Riko ta yayi da sauri ta fuzge zata shige daki, Inna ta kira sunanta, dole ta tsaya bazata iya share taba.
"Zonan ki zauna" Inna ta fadi hade da mata nuni da tabarma, jiki sanyaye ta zauna kanta na kallon gefe daban.
Zama yayi kusa da ita, "plz princess ki saurareni.
Dogon tsaki taja tare da dubansa tace "kaga malam idan ma kazo ne kamaida ni gidan ka you're mistaken, cox bazan bika ba, i'd rather die akan na kasance dakai, saboda na tsanake"
Murmushi yayi da jin kalamanta, mikewa tayi afusce tana fadin "ga mahaukaciya na magana dole kayi dariya" rikota yayi yace dawo ki zauna.
Zama tayi tanai buga mai harara.
      Yace "nazo ne amatsayin yayanki na jini ba mijin kiba, plz princess ki gayamin gaskia matan Baba nawa ?
Kallon rainin wayo tayi tace " Allah ya sauwake ka zama yayana, mugu kawai, kuma babu ruwanka dako matan Baba nawa"
"Dan Allah ki gayamin badan hali naba" ya fadi amairace.
Kallonsa tayi taga lailai ba wasa tattare dashi, saidai tambayar tai mata bambarakwai.
Tace "matan Baba daya, itace Maihaifiyata Hajjo"
Hannuta ya riko, kaman zaiyi kuka yace "princess ke kanwata ce ta jini, baban mu daya dake"
Kallon rashin fahimta tamai, gabadaya yasata duhu.
Yacigaba "apart from Hajjo wace mace ce kika sani arayuwar Baba ?
Shuru tayi tanai tunani tasan dai babu ko wace mace daga Hajjo sai ita, can dai ta tuna da wani abu tace "akwai mace daya mai sunana, saidai bansanta, Baban bai taba xancen taba, abakin Hajjo nima nasanta, idan nayi laifin takance halin ku daya da mai sunanki, wataran na tambayi Baba wace ce mai sunana, cewa kadai yayi baya fatan nasanta".
Kur yayi mata da ido, yace "Ci gaba"
"Shikenan abunda nasani"
"Plz princess try to remember wani abu
Bata rai tayi hade da dauke kai, tace "ni ba princess bace kadai na kirana da hakan".
Juyo da fuskar ta yayi yace "to mi you're a princess, sunan Momcy gareki kinsan bazan iya fadin sunan kiba".
Gabanta ne ya fadi adalilin kamshi gaskia data fara ganowa cikin xancen sa, sau da dama takan ga kamarsu da Baba saidai bata taba kawo komai aranta ba, kallon sa take tana son tuno wani abu, azubure ta mike tana fadin "OmG".
mikewa yayi hade da riko ta, tuni jikinta yahau rawa.
Cikin muryar kuka tace "you're right, kai yayana ne, what am not sure shine ba Mom ta haifeka ba, i tink Hajjo ta haifeka"
Sabon rudani ya shiga, yasan dai Mom ce uwarsa, yace "miyasa kika ce haka
"Hajjo once told me bani ce yarta ta fari ba, tacemin akwai yayana saidai ya b'ata baa gansa ba" ta fadi cikin kuka, rungumota yayi yanai lallashin ta, abunda dama yake son sanin wato su sibling ne, it doesnt matter ko wace ta haifesa, abu daya yasani shine Mom ce amatsayin mahaifiyar sa.
Kuka sosai take cike da tashin hankalin ya haramta gareta, sai yanxu tagane ashe tun asalin soyyayar jini ce ta hadasu take ta shirme da haukan son shi.
"Princess" taji tlya kira sunanta cikin wata kasalalliyar voice.
Kasa amsa mai tayi, tajanye jikinta gefe, kusa da Inna ta zauna hade da daura kai kan cinyarta tanai kara sautin kukan.
Tausayin su sosai Inna taji, ita kanta sharar kwalla take, matsowo yayi daf da ita yace "Baba suna kauye, gobe ki shirya sai muje can, ai kinsan garin ko ?
Girziza kai tayi alamun a'a bata san garin ba, asalima ma ko sunan kauyan bata sani ba, Jigawa state dai tasan kauyan yake, tun bayan da tana karama suka bar garin bata kara zuwa ba, alokacin ganin take idan taje kauyen yar kauye zata zama, su Hajjo da hassan ke zuwa ita kuma ta zauna gida tare ba baba dasu Hussaini, sai wataran kuma Baba yaje shi daya.
Baiyi Mamaki da rashin sanin kauyan taba, yasan xaa rini balle alokacin kanta na hayaki ba yanxu data saduda ba.
"Gobe zamu koma gida kinji?
Mak'e kafada tayi "nikam bazan bika gidan matar nan ba"
Yasan Mom dinsa take nufi, saidai bazai barta a zaria ba, yace "kiyi hakuri muje, banason  barayin nan na dazu su cafke ki"
Tsoro sosai taji dan tuni ta manta dasu, tace "gidan Baba xaka kaini"
"Ba kowa agidan, sabon gidan  Mardiyya xan kaiki ki zauna"
Fir taki yadda, saida Inna tasa Baki bayan ya zayyane mata abunda ya faru dazu Sanna ta amince zata bishi.

INA ZAN GANSHI ?Where stories live. Discover now