page 69 to 70

605 28 0
                                    

💖 *INA ZAN GANSHI*💖
            Rubutawa
                  Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

              69 - 70

Tsananin ranar daya k'walla garin bai hana ta ganin duhu da jin sanyi ba,
Tafe take tana lailayi sakamakon jirin dake neman d'ibar ta tsabar yunwa da radad'in da zuciyan ta yake, kuka take ba k'agauta, horn din motar dataji bayanta yasa ta daskarewa tsaye batare data waigo ba.
     Tuk'owa gaban ta yayi hade da wining glass kasa, hada idanu sukayi yanai kallon yadda idanuwanta sukaisauya launi zuwa ja, kawar da kai yayi ya ciro d'ari biyar daga wallet  dinsa, cikin rashin damuwa da yanayinta ya cilla mata kudin afuska yabai wa motar wuta yayi gaba.
     Yak'en da yafi kuka ciwo tayi hade da sa hannu tadau kudin da tuni ya fad'i k'asa, jinjina kai tayi, tana xancen zuci, ko mi yay mata bataga laifin sa ba ita ta jama kanta, asalima sonshi ba raguwa yayi a xuciyan taba idan ma ya dawo gareta hannu bibbiyu xata amshe sa, saidai ayadda taga fuskar sa she doesn't tink xai k'ara waiwayanta, kuka sosai take tana consoling kanta, tasan Mamuda nada kirki da kyakyawan zuciya  baxai share taba, he will definitely come for her.
    Hope sosai tayi ta bawa kanta, taxi ta samu ya dawo da ita gidan sanna ta biyasa da dari biyar din.
     Marwa tagani tsaye gaban gidan, yana zuba yan tarkace a gidan baya, da azama ta shige gidan sanin cewan tarkacan Inna ne.
   Tsaye taga Inna bakin kofa tana kokarin datsewa da k'wado, dan ihu mai tattare da tashin hankali tayi tana fadin
"Inna karki tafi ki barni"
Sai sannan Inna ta ankara da ita, sosai Batul ta bata tausayin sakamakon fita hayayyacinta da taga tayi.
"Batula kin dawo ashe" Inna ta fadi hade da zare mukillin k'wadon.
Karasawa gabanta Batul tayi ta tsugunna, cikin kuka tace "inna dan Allah ki zauna dani, bansan ina xan nufa ba, Mamuda ya sakeni ko kuma ince RMd ya sakeni dan nasan kinsan komai"
Dagota Inna tayi tanai kallonta.
"Batula laifin kini ai, kwanaki ba yadda ban rokeki karki tafi ba kikayi kunnan uwar shegu kika kara gaba, inda ace kin tsaya da Rasheed bai sake kiba, aranar yaso bayyana maki kansan amma ke kika tafi nuna mai kanki"
Sosai take kukan tace, "nasan na tafka babban kuskure, amma Inna ai bai kamata ya sakeni ba kodan son dana kemai"
Goge mata hawayan Inna tayi.
"Kidaina kuka, Allah yasa sakin yafi alheri, yanxu
Ki dau kayanki ki koma gidan ku"
Kai ta girgiza, "Inna tsoro nakeji bazan iya komawa gida ba, ki temaka ki zauna dani kafin wasu kwanaki saina koma gida inyaso muje tare ki tayani bawa Baba da Hajjo hakuri"
Ajiyar zuciya Inna ta sauke tace "kinga ni baa garin nan nake ba, Jikana ne abokin rasheed shiya kawoni nazauna dake na dan wasu lokuta, yanxu kuwa gida xan koma Zaria na cigaba da sana'ata shiyasa kika ga na dawo daukan sauran tarkace na"
Kyankyame Inna tayi tana rokonta, "dan Allah kije dani Zaria, ko talla ce xan miki, Inna ki temaka.." Karashe maganar tayi cikin matsananci kuka.
Ba karamin tausayinta Inna taji ba, tace mata ta dauko kayanta su tafi, cikin rawar jiki Batul ta fada daki ta warb'o ghanar ta fito sukayi waje, Marwan suka shiga yajasu zuwa tashar kawo suka shiga motar Zaria.

        *Kauyen Marke*

Jigawa state.

Zaune Hajjo take a tsakar gidan su mai zagaye da kara masu kauri, Rike take da rariya tana tankadar garin masara. Shigowa baba yayi yanai wa su Hassan nuni da inda zasu ajiye buhun albasar dake lafce bisa bayansu, ajiyewa sukai hade da sauke numfashi.
Zama Baba yayi bisa tabarma dake shimfud'e, Hajjo tamai sannu hade da mikewa bakin randa dibo mai ruwa.
"Noma akwai dadi, kaman karmu koma Kaduna" Hussaini ya fadi yana zama kan tabarmar.
Hassan dake tsaye yace "nikam na matsu mu koma naga Batula"
Guntun tsaki Hussaini yayi.
"Batula ta manta mu, tunda tayi aure bata kira kosau daya ba, gashi ita layinta baa samu, na tabbata arziki tayi ta yashe mu"
Kwafa baba yayi yace "banason gulma, ku tashi ku bani waje".
Tsum suka mike suka fice,   takaici ne yakama Hussaini, ya dade da lura duk cikinsu Baba yafi son Batul, sau da dama tayi laifi baya hukuntata saiko Hajjo ta mata duka amma su abu kadan yahau masu fada, shiyasa sam Jinin su bai hadu da itaba dan kuwa bayason raini dukda ita din yayar shice.

INA ZAN GANSHI ?Where stories live. Discover now