Babi na uku

233 24 25
                                    

SANADINKI NE!

BABI NA UKU
Saifullah Usman Galadima wanda aka fi sani da Saif ko kuma ( S.U.G ) . Mutum ne wanda baya son hayaniya ko kad'an . Tseye yeke yana kallon tagan d'akinsa ba abunda  ya tsana kaman kukan tsuntsaye da sharan zakara. Wasu kaji  ne da tanta'baru suka addabeshi, Tun tarewansa a gidan sati biyu da suka  wuce.  Duk da ginin gidan , gini ne na bene kuma dakinsa a sama yeke . kajin nan haka zasu fire  zuwa sama don naci da jaraba,  bai san kuma me zaiyi musu su tafi ba, kaman suna da masaniya duk d'akin da yaje ya kwana sai sunje ta tagan sun ta damunshi da kukansu , bai ma san daga ina suke zuwa ba , gabaki daya yama rasa yanda zaiyi dasu. Ba ranan da garin Allah zai waye basu zuba shi kuma ba ranan da ba ya koransu amma  washegari haka zasu sake dawowa. Abun mamaki kuma ya kasa sabawa da kukan su, wani lokacin har kofa zai bude  yaje ya koresu, wani lokacin kuma ya dinga bude  window yana rufewa ko zasu gudu, amma  ko a jikinsu . Shi da gidanshi sun hanashi baccin tsafiya. Gashi kuma shi mutum ne mai son  baccin tsafiya  . kaman yayi kuka ba yanda ya iya hakan ya hakura. Yaso yin bacci ko da kad'an ne domin kusan kwanakin nan duka baya iya baccin kirki . Ganin yana  'batawa kansa lokaci gashi har karfe shida tawuca  yasa ya shirya  zuwa mini Gym .  kasancewansa mutum ne mai son motsa jiki . Har wajen motsa jiki ya gyara a gidansa.
******

Khaleel ne yashigo cikin gym d'in . “ Ango kasha qamshi gwomma ka kara himma wajen shaping na jikinka kada amarya tafara  complaint kasan  mata dason maza  masu  exercise, ” harara ya watsa masa ,“ meya  kawoka ba tun  jiya na sallameka ba. ” murmushi yayi “ kad'a kadamu mutumina in na kawo ma amaryarka zanyi  gaba .”  Hannu khaleel ya miqa masa alaman su gaisa “ Assalamu Alaikum. ” kamar wanda bayason  amsa sallaman ya mika masa hannu. Murmushi khaleel yayi tunawa da yanda suka  rabu da mutumin nasa jiya. Gashi har yanzu yana wani cin magani don kad'a ya tada maganan jiya, dole ne su masa magana ya rage yawan fushi da yawan hada fuska. Saboda in yayi aure matar tasake jiki dashi  .
“ Yakamata Saif zuwa yanzu ka girma ka daina  yawan fushi.  mufa nasiha ne kawai muke  maka a matsayin mu  na elders wanda muke da aure, kasan  abun sai anhada da tips ” Saif dai bai ce masa komai ba sanin halin  khaleel da son girma don haka Towel kawai yaja  ya fara goge zufan dake saukowa daga jikinsa. Khaleel na binshi har suka  isa kitchen , yaso watsa  ruwa a jikinsa , amma  yunwa yakeji don haka Coffee kawai ya hada  ma kansa , ya cewa khaleel , “suit yourself ,” murmushi kawai yayi “madam ta cikamin ciki da masa da kunun gyada , kada kadamu mutumina.”
*****

Yana gama shan coffeensa wayansa ya fitar  yafara game .  khaleel na ganin haka yafara magana “ na dauka  wanka  zakayi mushirya zuwa main house kasan ana jiranmu ashan , gashi ka hana  mutane zuwa gidan nan ban san  daga ina ka kawo wa'anan securities ba nima sai da nayi tsiya da su ba kadan   kamun  inshiga gidan nan yau, wai kabada order kada kowa yashi go ” ganin saif bai ce masa komai ba .
“ Saif wai ni kam  bada kai nake magana, tun  dazu ina ta ma bayani ko ka d'aga ido kagan ni,” kanshi kawai  ya daga batare da  yace komai ba ya zubawa d'an uwan nasa 'kyawawan idanunsa da ke rikita  mutane dayawa. Hannu ya masa alaman me ka ke cewa ne. “ Kasan Allah bana son rainin hankali kana ganin karfe  takwas har tayi. Kuma kana sane daurin auren nan sha d'aya ne . ”  Hararan da saif ya zuba masa  ne ya bashi dariya “ kaga Malam ni dai taya ka shiri kawai nake yi , kasan assignment aka bani, zanyi kokarin ganin nayi aikina  yanda aka bani umarni. ” Kai kawai Saif ya girgiza masa da motsin da yayi da bakinsa . Yasa ya gane meyeke  nufi waton cewa shi ba inda zai je . Daga hakan  ya maida hankalinsa zuwa wajen game da yeke yi da wayansa . khaleel na ganin haka yasan Saif bai da niyyan shiri.  Bai kara ce masa komai ba ya fito daga parlour. Yana tafiya yana tunani mutum d'aya kawai zai iya da Saif kuma tana busy yanzu .  Allah ma yasani, shi  yana tausayawa matan da Saif  zai aura , shi yasa ma bai so wannan auren da za'a ma dan uwan nashi din. Sanin halin abokinshi dan uwanshi,  kuma surqinsa  tun  tasowansu shi wani  irin mutum ne da gane  halinshi sai a hankali . Haka ya sake koma parlourn babu  yanda ya  iya dole ne yayi hakuri don rana d'ayan  nan ko da lallashi ne in ya kama yayi zai yi  in dai bukatan iyayensu  zai biya Zai yi don ya samu kan Saif din. In ba haka ba Nana zata iya fushi dashi tunda ta bashi wannan aikin .
********

Ko da khaleel ya  dawo bangaren  Saif bai tarar  dashi a  parlor ba.  don haka ya haura zuwa sama , yayi sallama yaji shiru , sai ya bud'e  dakin Saif ya duba dakin , shima bai tarar  dashi ba har zai  juya ya fita  yaji kaman motsin ruwa  a bayi murmushi yayi yasan Saif na wankane. Don haka ya sauko  zuwa a dai_dai lokacin kuma wayansa  yayi ringing. Abba ne ke kiransa.

  

Saif dai ba abunda yeke  yi a toilet sai tsaki , Allah ma ya tsani shi baya  yadda da kowa more especially mata. Yasha yadda da mutane amma a  karshe  cutar dashi suke yi . Shi yasanya baya  son soyyaya a rayuwansa domin ba abinda ke cikinta sai wahala da yaudara. Ba yanda ya iya ya zama dole yayi biyyaya wannan karon,  ya auri zabin Iyayensa ba don yaso  yin haka ba.

Dada Sukabe ce!👌🏻

SANADINKI NE ! Donde viven las historias. Descúbrelo ahora