★★★★★★
       *_SIRRIN ƁOYE_*
                       ★★★★★★


              *_NA_*

*_UMMA MUHAMMAD NAJAMAGA_*


🅿️14



*_FREE PAGE_*

         *_Am repeating my self book ɗina  na kuɗi ne if you read without paying is your own cup if tea_*

*_my book is very cheap Naira #200 only you can transfer your card through this number 08146405540, or transfer through  this account number, 3053905686,UMMA MUHAMMAD POLARIS BANK show your evidence of payment through this number 08146405540_*

Doctor Saleem ne zaune shida yarima Almustapha.

       Gaba ɗayan su ido suka bita dashi  suna kallon ta cike da mamakin wacece ita..

Gaba ɗaya yarima idon shi nakan ƙirjin ta domin saman nipple ɗinta ne kaɗai baa gani.

       Sai yanzu ya Lura da kalar jikin ta.

Masha Allah ya furta a cikin ranshi domin kwalli da yayi da colour ɗin ta wato chocolate.

      Gwanda yarima na cikin nutsuwan shi Amman shi doctor Saleem Bai ma San inda kanshi ba yake.

      Miƙa tayi ta turo ƙirjin ta waje.

Ai doctor Saleem Saida ya dafe hantsar wandon shi.

    Ita hidimar gaban ta take bama ta kula dasu ba.

  Shi yarima Almustapha tun daɗewa ya dawo cikin nutsuwan shi Amman doctor Saleem ina.

       Maganar gimbiya ce ta dawo da kowa daga zancen zucin da ya tafi.

"Yawwa doctor Saleem Ashe ka ƙara s......"

      Maganar ta ce ta tsaya cikk tana kallon Almustapha cike da mamaki.

    Ko kallon inda take bayyi ba.

Da mamaki ta ƙara so gurin su ta zauna.

     Itama sharewa tayi domin a yanayin da tagan shi yana iya mata wulaƙanci a gaban doctor Saleem.

Da murmurshi akan fuskan doctor Saleem yace.

      "Ranki ya daɗe Ashe kin dawo to ya hanya?."

Itama murmurshi tayi sannan tace.

       "Alhamdulillahi doctor ya aiki.?"

Shima da fara'ar a fuskan shi yace.

     "Lafiya qlw Amman nayi mamakin ganin ki? Keda mukayi dake sai next week zaki dawo ?."

Itama dariya tayi sannan tace.

      "Ba dole ba in dawo inje Ina can ayiwa mijina madadi da wata."

Dariya doctor Saleem yayi sannan yace.

      "Haba gimbiya kina bani kunya wallahi,kina ƴar sarki Amman kike tsoran kishiya, haba dai nasan kowa za'a auro baza takai ki nasaba ba."

  "Hmm doctor bazaka gane ba, tabbas bani son kishiya Amman abunda nake gudu shine a aurawa mijina baiwa, cabb wannan abun bazai taɓa yiyuwa ba wallahi Ni kaɗai na dace da mijina tamkar yadda aka halicce shi Danni kaɗai."

      Murmurshi doctor Saleem yayi sannan yace.

"Gaskiya gimbiya ki rage tsoran kishiya."

      "Kaga doctor mu bar wannan zancen bashina Kira kaba."

Shima gyara Zama yayi Amman duk wannan maganar da yake hankalin shi nakan Aminatu.

       "To aini nagama duk abunda da zanyi kawai ke nake jira dafa tan an dace ?."

      Murmurshin tayi irin na nasara ɗinnan sannan tace.

"Alhamdulillahi ai angama dacewa insha Allah around 8:30 o'clock zamu zo."

      "OK Allah yakawo ku lafiya."

"Ameen."

Fita yayi daga gidan Amman dukkan hankalin sa yana kan Aminatu.

     Aranshi yake raya sai bayan wannan abun zaiji wacece gaskiya tatafi da imanin shi.

Duk wannan abun da suke yarima yana zaune yana danna waya ko kallon inda take bayyi ba.

      Tana zuwa ta faɗa jikin shi .

Kukan shagwaba ta sanya mishi.

   Ga mamakin ta ture ta taga yayi ya tashi tsaye.

     Itama cikin mamakin take kallon shi.

Duk yanda takai ga tsiyawa Amman ganin fuskan yarima a haka Saida gaban ta ya faɗi.

       Cikin ɓacin rai yafara magana.

"Wato Dan kinga na damu dake shine har rashin mutunci yafara tashi daga kaina da mutanan gidan nan ya koma cikin ma'aikatan masarautar nan ko ?."

     "Ni bazan ce miki komai ba kije shugaba nasan ganin ki, ki karɓi hukunci daidai da abunda kika aikata."

      "Allah yasa hukuncin da zata miki ya shafi zaman mu tasa na ƙara aure ko kuma ta rabamu saboda banyi dacen mata ba."

     Yana gama maganar ya fice daga gidan gaba ɗaya.

Jikin gimbiya Banda rawa babu abunda yake.

     Lalle ta yarda takai yarima ƙarshe .

Cikin sauri ta sanya alkyabbar da tacire.

     Kallon Aminatu tayi sannan tace.

"Wuce muje can wallahi na yarda komai ya faru Dani Amman Banda Abu biyu.."

      "Kishiya."

"Mutuwar aure."

   Dakyar ta nutsa kanta suka nufi part ɗin gimbiya.

     Kallon da tafara mata Saida hanjin cikin Aminatu ya kaɗa bare gimbiya.

Gaida shugaba tayi Amman dukan su babu ta wacce ta amsa.

Magana shugaba ta farayi cikin ɓacin rai.........


*_SAURAN ONE PAGE FREE PAGE YA ƘARE_*

SIRRIN B'OYEWhere stories live. Discover now