33-34

155 6 0
                                    

🌳🌳🌳🌳🌳🌳
        🌳🌳
*GྂUྂDྂUྂ Aྂ JྂEྂJྂIྂ*
🌳🌳🌳🌳🌳🌳
           🌳🌳

*₴тояу щяїттёи Ьу*

*ᏃᎯᏂᖇᎯ ᎯᏰᎴᏌl{mᏫm ᎯᏂlᎯᏁ}*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*fílín gαíѕhє gαíѕhє zαn gαíѕhє dα mαѕσчαnα gudu α jєjí dαmα ѕαurαn grσup'ѕ kαmαr hαkα*............

*ѕαí α nєхt pαgє zαn fαdí ѕunαчєn ku kunα rαínα αlwαчѕ*❣

Short story✍🏻

*بسم ا لله لر حمن لر حيم*

🅿-3⃣2⃣➡3⃣3⃣

Dad babu kalan neman sameer da baiyi ba amma bai gansa ba har aka koma gida

Su amare zaune adaki bayan  su dad sun dawo ne ake shaidawa mutanen gida an. Ɗaura aure lpy  wasu ƙawayen da suke waje  sukaji da gudu suka koma daki domin su shaidawa amare an ɗaura aure

Da gudu suka shiga dakin suna murna cike da zolaya sukace masha Allah aure ya ɗauru gam ba rabuwa insha Allah

Wani faduwan gaba ne ya zuyarci zuciyoyinsu nan suka shiga kuka
Ƙawaye suka hau basu baki haba dan Allah kudai na wannan kuke kuken saika ce gidan mutuwa ba gidan biki ba

A yau fa kun taka matsayin da duk wata mace mai hnkln da tunani takeson takawa gdy ya kamata ace kunyiwa ubangiji ba kuka ba

Wata tace saidai idan kukan farin ciki kukeyi dry suka saka amma banda amare dake kuka basu bari ba

Ihsan a zuciyarta tace uhum ba gwanda ma su safreena da madina ba auren soyayya ne dama akwai shiri ni mai lkc daya kuma nace mene ai na boni wlh addua tashiga yi a zuciyarta Allah yasa auren ya zamto Alkhairi agareta ita da mijinta Allah kuma yasa yasota koda kaɗan ne

Dad ne ya turawa sameer text message *KA SAMENI A BEDROOM DINA*

Sameer dake kwance adaki yana jin zafi a zuciyarsa roqon Allah yakeyi Allah ya sassauta masa son matar wani domin yanzu ita haramiyarsa ce

Astagfirullah shine kawai abinda yake iya nanatawa a zuciyarsa saqon dad yagani saida ya gyara fuskarsa ya saita natsuwarsa kafin yafito baiga su khalifa ba azuciyarsa yace to ina sukaje ko dai an haɗa reception ne

Yanata tunane tunane harya fita jama'a ne yagani fal aciki da wajen gidan ga maroƙa suna wa'sa dad ya auren da yara maza uku a lkc daya sai fatan Allah ya ƙara girma suke masa

Yama rasa tayaya zai fara bin ta cikin wannan  jama'ar

Yace yauwa bari nabi kofar baya
Nan ma yaga ashe akwai mutane nan suka shiga yimasa fatan alkhairi suna tayasa murna

Murmushi ya kwaƙulo yanayi yana daga musu hannu harya samu yashiga part din dad

A bedroom din ya samesa yana zaune yayi sallama dad ya amsa ba yabo ba fallasa

Zama yayi a ƙasan carpet ya duƙar da kansa ƙasa yace dad gani

Dad yace ina kaje bayan an ɗaura aure ban ganka ba cikin sanyin murya yace kayi hkr dad zazzabi ne ya rufeni shine nadawo gida nasha magani

Dad yace sameer na isa da kai ko ban isa da kai ba? tmbya ce kabani amsa

Gaban sameer ne ya fadi yace
dad ka isa dani

GUDU A JEJIWhere stories live. Discover now