PAGE 71_76

108 10 12
                                    

[2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
             💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

  *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH  ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___71💎

    Sunana Nuraddeen Idris Aliyu wanda akafi sani da Dr N.I Aliyu wato qwararren likita a fannin lafiya daya shafi matsalolin qwaqwalwa...

Waro idanuwa Rashida tayi had'e da qurawa masa idanuwa cike da farinciki, alokaci d'aya tashiga qwalawasu Fatima kira, aunty, aunty, aunty kufito kuzo kugani ga abban little a tv ana fira dashi, pls aunty kufito kugansa, habiby ne wlh, kufito don ALLAH kada agama firar dashi.

Tadinga fad'a tana k'walamasu kira, ayanda take kiran nasu yasasu fitowa da sauri ba shiri, musamman Dr. Nura har yana shirin fad'uwa sanadiyar tuntub'en da yayi, ita kuma Fatima daqyar take takawa saboda nauyin da tayi, gashidai girma nadad'a tarar masu amma har lokacin haihuwa bata tsaya masu ba tasamu daqyar ta qaraso ciki, Saida takai jikin tv tasa yatsa adaidai gefen da aka nuno hotonsa tana fad'in uncle wannan shine mijina, shine abban little aunty,

Dawowa tayi tariqa Fatima tana cewa, kuzauna aunty kusaurari firar da za'ayi dashi, gaba d'aya ya canza saida nakallesa da kyau da sunan sa daya fad'a sannan zuciyata ta gamsu da cewa shid'inne, taqare maganar had'e da zaunar ita saman kujera, kaima uncle kazauna tafad'a lokacin da take qoqarin zaunawa itama had'e da qura masa ido, wani irin farinciki take jin kanta aciki marar misaltuwa, addu'a tadingayi azuciyarta akan ALLAH yasa yafad'i cewa zai dawo garesu nan kusa bada jimawa ba,

Wayarta tajawo ta lalubo lambar umma lokacin tarako dady zai fita riqe da hularsa tana yimasa addu'a, kasancewar wayar na nan falo saman kujera yasa umma tad'auko tare da d'agawa, Saida tayi murmushi sannan tace Rashida kuna lafiya, cikin zumud'i ta amsa mata tana cewa umma ku kunna tv a tashar BBC ana fira da mijina, gaba d'aya tamanta da umma take magana saboda hankalinta gaba d'aya na wajen firar da akeyi da Nuraddeen yana bada amsa, jin da tayi umma tayi tsaki had'e da cewa marar kunya yasa takashe wayar tana girgiza kai yasa tayi saurin toshe baki tana dariyar da da zaran ka kalleta zaka fahimci tsantsar farincikin dake tattare da ita taci gaba da kallonta

Dady ne yatambayi umma ko lafiya yaga tayi tsaki, tace kabarni da yarinyarnan marar kunya wai ni take fad'awa na kunna tv tashar BBC ana fira da mijinta inba tsabar rashin ta ido ba sai kace mijin nata yadamu da itane, dariya yayi tare da matsawa ya d'auki remote d'in tv dake kunne yana fad'in, to meye abun kunya aciki, idan bata fad'a maki ba wa kikeso tafad'awa?, ko Qaryane tafad'a shid'in ba mijinta bane? yaqare maganar daidai lokacin da yakamo tashar BBC, juyawa tayi zatabar wajen don batasonma ganinsa gaba d'aya dady yariqo hannunta had'e da cewa don ALLAH tsaya suji ko zasu samu wata hujja acikin firar da akeyi dashi wacce tahanasa dawowa, dama tuni ita umma tafara jin haushinsa tun lokacin da suka tsinci labarin cewa yace bazai dawo qasar ba yafiso yayi zamansa acan, shene abun yaqona mata rai har take ganin kamar yayine don yacutar mata da yarinya data kafe kai da qafa saishi duk da yashafe shekaru masu yawa acan batare daya tab'a tunanin waiwayo taba.

Babu yanda ta iya dole suka zauna suna kallon fira.

Gaba d'aya b'angaroran biyu sun shagala da irin firar da akeyi dashi har zuwa lokacin da ake tambayarsa dalilin daya hanasa komawa qasarsa yabada gudun mawarsa duk da zamowar gwamnatin qasarce ta d'auki nauyin karatunsa da komai nasa har zuwa lokacin daya kammala, yajima shiru yana tunanin amsar da zai bayar amma daga qarshe yace bayada wani dalili, kawai yafi sha'awar yayi zaunensa acan ne, da aka sake tambayarsa cewa ko yayi hakanne saboda kud'in da can qasar za'a bashi anan qasar baza'a tab'a iya bashi koda makamancinsu bane amma bud'ar bakinsa sai cewa yayi koda qasar bazata biyashi ko sisi ba yafiso ya zauna acan, shi kawai baisan abunda yasa hakanba amma yafi son zama acan har iya qarshen rayuwarsa fiye da yakoma qasarsa.

SANNU SANNU Bata Hana zuwa..Where stories live. Discover now