PART 9, page 46-50

170 12 1
                                    

[8/4, 11:16 PM] FARI'S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
             💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

  *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH  ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

_Alhamdulillah for d unlimited bless anytime ya rabh👏 hi sister's gaisuwa tare da fatan alkhairi ga d'aukacin masoyana kuma masoyan littafin SANNU SANNU... Ina yiwa kowa BARKA DA SALLAH tare da fatan anyi sallah lafiya,🥰 ubangiji ALLAH ya maimaita mana kasa ni daku munyi tarayya acikin d'imbin ladaddaki da gafarar ALLAH dake cikin wud'annan kwanakin da suka shud'e,👏💃🏼 ALLAH kajiqan dukkanin iyayenmu wud'anda suka rasu da wud'anda keraye Kuma kabasu aljannah da rahamarka damu baki d'aya👏 Ina fatar zamu d'ora daga inda mukatsaya kuma zaku bani 'yan barka da sallah ta tunda rowar nama tasa kun b'uya ko leqowa bakwayi a group balle atuna da littafin SANNU SANNU sai yanzu da kuka cinyye abunku,🥰😅 SANNU SANNU fans group 1&2 ina jiran 'yan barka da sallahta😅😅😅hohoho..ku kwantar da hankalinku kud'i nake so ni ba nama  ba don naga wasun ku sun fara hararata, to bashi nake so ba amma dai kuci ahankli ko ince wacce duk ta zaqe da yawa ALLAH yasa tafara z....🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🤣🤣🤣🤣ahhh to bandai iyar ba balle ace Billy tayi muguwar addu'a. *LUV YOU ALL FILLAH* ❤️_

Page___46💎

     Tun da sassafe baffa yakira inspector najida tayi masa bayanin bayanan da suka samu a hannun yaya hawwa tare da tabbatar masa da cewa yau d'innan zasuje da ita har dajin da bokan yake shima aka mosa, matsala d'aya basuda tabbacin kamosan zaisa asan inda yarinyar take tunda harkace ta shed'anin aljanu, kawai zasuyi hakanne don yazama izina uma tudun da zasu dafa wajen ganin sun kauda masu munanan halaye irin na Yaya hawwa da bokan, saboda Haka ta shawarci baffa da kawai atashi tsaye da addu'a in sha ALLAH ALLAH zai bayyanata, sosai baffa yaji dad'i akan matakin da tace zasu d'aukar masu, ad'aya b'angaren zuciyarsa kuwa halin yaji yasamu wata 'yar qaramar natsuwa don yanada tabbaci akan yanda Rashida tayi riqo da addininta ALLAH bazai tab'a Bari acutar da ita ba, saidai idan yaso ya jarabce tane daga cikin jerin qaddarorin daya tsaro mata arayuwa,  godiya yayi Maya sannan ya kashe wayar, daidai lokacin Nuraddeen yafito wanka riqe da d'an qaramin towel yana goge jikinsa, kallonsa baffa yayi cike da tausayi lokacin daya hau shirya kansa kafin yace.

"Nuraddeen Ina zakaje ne haka tunda sassafe?."

"Yarimawa." Yabashi amsa ataqaice yana qoqarin zura rigarsa ajiki, "ehmm!..to Bari na shirya sai muje dama Ina son inje dubo aminina, jiya da muka had'u da malam balarabe akasuwa take fad'amun cewa har anba iyalin tasa sallama, kwana biyu banje ba saboda akoyaushe idan muka had'a idanuwa dasu tausayinsu kanjefani cikin matsananciyar kunya da damuwa, maganar gaskiya mahaifiyarka Bata kyauta ba, ta matuqar cutar da rayuwar wud'annan bayin ALLAH."

"Zan nema Maya tafiyarsu baffa, ALLAH kayafe Maya Kuma ya shiryar da ita damu baki d'aya, jarabawar innar mu ce tazo mata ahaka wacce dukkaninku bamu wuce tab'a awurin ALLAH, fatanmu d'aya ALLAH karya jarabcemu ta irin hanyar da aka jarabtata," ajiyar zuciya baffa yayi yana kallon Nuraddeen, tabbas gaba d'aya halayensa na sanyin hali ya d'ebo amma anan harya zartasa tunda take kallon son zuciyar mahaifiyarsa a matsayin kuskure da jarabawar rayuwa, sab:'anin shi dake kallon abun a matsayin mugunta, rashin imani da kuma rashin tausayi, murmushi yayi yana godema ALLAH daya bashi d'a k'waya d'aya tamkar da dubu kafin yace.

"Amin Nuraddeen, bar na watso ruwan nima, idan baffanka yazo kace masa yajirani sai muje tare ko?"

"To baffa" yafad'a had'e da zaunawa gefen katifar dake cikin d'akin yana d'aure zaren takalminsa daya saka yanzu, azahiri idan ka kallesa cikin natsuwa zaka fahimci fuskar a sake take ba yabo ba fallasa amma acan cikin zuciyarsa akwai d'imbin miki da damuwa a cunkushe da ita, yana nan zaune baffa usman ya shigo shida Yusuf d'auke da kayan karin da aka Saba kawo masu, da sauri Nuraddeen yamiqe yana gwadawa baffa Usman gefen katifar  daya tashi akai tare dasa hannayensa ya dafa kafad'un Yusuf yana fad'in.

SANNU SANNU Bata Hana zuwa..Where stories live. Discover now