part 3

481 17 2
                                    

[6/19, 9:17 PM] FARI'S DOTA💎💃🏼: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___11💎

Gyaran murya baffa yayi yana kallonsu baba kafin yace,

"Malan bashar nasan kai kasan wannan" yana nuna d'an nasa sannan yaci gaba da cewa "don haka Babu buqatar in sake gabatar maka dashi saidai ko in wud'anna 'yan uwan nawa, amma ku su alhaji surajo, malan hashimu, sa'idu, malan shu'aibu da malan balarabe ga d'anku nan Nuraddeen wato d'an wajena koda ALLAH zaisa wata rana a had'u zaku iya ganesa shima yagane ku, wud'annan su biyun da kuke gani kuma qannena ne uwa d'aya uba d'aya wato Usman da aliyu, inafatar ko bana raye ace abota da kuma mutuncin dake tsakanina daku bai yanke ba, inaso ya zamana cewa idan anhad'u da juna za'a iya gaisa har kudinga tunowa dani kuna yimani addu'a"

"Ashsha malan idi! don ALLAH kadena fad'ar haka domin ita cuta ba mutuwa bace, mudai fatanmu d'aya shine ubangiji ALLAH yabaka lafiya kuma ALLAH yaraya manasu shi da sauran 'yan uwansa ya tashi kafad'unka acikin iyalinka." Haka suka dinga fad'a tare da yimasa addu'a,

Shiru baffa yayi yana kallonsu d'aya bayan d'aya nan take yaji wasu hawaye sun cika masa idanuwa, tari yafarayi wanda hakan yabawa hawayen dake maqale a idanuwansa damar zubowa, sannu duk suka dinga jero masa cikin jin k'warin guiwa ya kaikaita idanuwansu yana goge hawayen had'e da amsa masu,

Bayan tarin ya lafa masa ya maido kallonsa ga 'yan uwansa da kuma d'an nasa suma ya gabatar masu da aminan nasa inda har yak'ara masu da cewa shi awajensa abokan nasa sunfi qarfin yakirasu da abokanai ko aminai saidai yace sud'in 'yan uwan sane shaqiqai, don haka yana roqonsu dasu riqesu hannu biyu bisa kyautatawa da kuma girmamawa, gaba d'ayansu ji sukayi jikinsu yayi sanyi saboda yanayin yanda yake magana tamkar wanda ke barin wasiya, murmushi yayi ganin yanda fuskokinsu suka canxa had'e da cewa "kada kusaka kawunanku cikin damuwa akan maganganun dake fitowa abakina domin natabbata daga cikinsu akwai wud'anda zasu sanyaya zuciyoyinku kuma su sakaku cikin farinciki marar misaltuwa" juyowa yayi inda d'an nasa me zaune yace, "Nuraddeen tashi katafi, ALLAH yayi maka albarka" ajiyar zuciya malan Idris ya sauke had'e da mik'ewa tsaye yad'an sunkuyar dakai agabansu alamar girmamawa sannan yafice daga d'akin,

Bayan yafita baffa ya kalli 'yan uwansa yace, "usman, Aliyu Ina son kunemawa d'anku Nuraddeen izinin neman auren Rashida 'yar gidan malan bashar a hannun iyayenta dake zaune agabanku idan har ba'a tsayar mata da miji ba kamar yanda d'annaku yabuqata cewa yana sonta"

Wani irin annurine da farinciki ya bayyana a fuskokinsu gaba d'aya jin kalaman dake fito daga bakin aminin nasu in banda baba da kuma aliyu qanen baffa, shidai baba tsantsar farincikine da kuma mamakin jin cewa wai malan idris nason 'yarsa Rashida, shikuma Aliyu tsananin bak'inciki da takaicin hakanne da yaji yasa yakasa b'oyewa saboda 'yarsa muneera yaso ya had'a aurensu da shi saboda yanda take tsananin sonshi. Sosai baffa yalura da sauyawar fuskar da d'an uwansa tayi Amma sai ya basar saboda jin Usman na fad'in "Masha Allah, alhamdulillah, agaskiya haka yayi kyau kuma shizai k'ara dank'on zumunci a tsakaninmu, don baka iyayen rashida kunji buqatar d'anku idan har yarinyar nan ba'a tsaida mata da miji ba, to muna nema masa izinin yafara zuwa wajenta donsu daidaita"

Gaba d'ayansu suka had'a baki wajen cewa, "to aimu da Nuraddeen da Kuma Rashida duk 'ya'yanmune, saboda haka indon ta tamu bamuqi jinin yau a d'aura masu aure ba, don haka mu tabakin malan bashar muke jira sai muyanke hukunci"

SANNU SANNU Bata Hana zuwa..Where stories live. Discover now