PAGE 81-90

140 11 11
                                    

[2/13, 10:36 PM] Mmn Queen: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
             💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

  *DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH  ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___81💎

    Duk iya qoqarin da baffa Usman zaiyi awajen don ya gamsar da baffa cewa Nuraddeen ba'a bisa hankalin kansa yaqi dawowa qasarsa ba qinyarda yayi daga qarshema ya shashantar da maganar tahanyar yiwa baba balarabe da shima yake had'a baki da da baffa Usman wajen qoqarin lurar dashi nuni da kwanon furar dake gabansa yana fad'in.

"Bisimillah malan balarabe kasamu ko furar ce kasha maqoshinka yabud'e sannan kaci abinci tunda naga nema kake ka ida dallashesa bayan kukan da kasha." Yaqare maganar cikin zolaya gaba d'aya sukasa dariya.

'Daukar kwanon furar yayi yasha sosai har saida yakusa shanyewa sannan ya ajiye baffa yace.

"Yawwa ko kaifa, yanzu fad'amun ya labarin 'yatah Rashida da mahaifiyarta?, Suma suna fushi damu ko?"

"Gaskiya banace haka ba, Amma dai ita mahaifiyarta taji ba dad'i sosai musamman da yarinyar taqi amincewa da hukuncin da shi mijin mahaifiyarta yayi yunqurin d'auka naganin yazo in akwai hanyar da za'abi don samun maslaha abi idan kuma babu sai aje kotu taraba auren, acewarsa bazai yuyu ta zauna da aurensa ba kuma bayanan."

"ALLAH sarki, dole zataji hakan ai, abubuwanne sunyimata yawa akai, Kuma bai kamata abiyewa ra'ayin yarinyar ba tunda ko musulunci bai yarda da hakan ba, kaga dai har yau babu wanda aka cutar acikin wannan al'amarin kamar ita Rashida, mtsss kwata kwata wannan abun beyi dad'i ba, wlh da anje kotun anraba auren da duk sai yafi akan wannan zaman da tayi tab'ata quruciyarta gaba d'aya ga wanda baisan darajar aure ba."

Baffa yaqare maganar cike da damuwa d'auke a fuskarsa, bashar (Abba) ne yashigo shida yayunsa asiya da Bilkisu riqe da jikunkunan littafansu na leda zasuje islamiya baba nusaiba tabakkasu abinci ga kwano sukawowa Yaya hawwa, kasancewar shine agaba yana hango baffa yarugo yafad'a ajikinsa, nan take duk damuwar dake tattare afuskar baffa ta b'ace ya d'agosa cike da fara'a yana fad'in.

"A'a aminina har anfito zuwa makarantar?"

"Eh baffa, Ina wuni?"

"Lafiya klw aminina, injin babarku tabaka abinci kaci ka qoshi." Yaqarasa maganar yana dariya tare da d'an mammatsa cikinsa.

Dariyar shima yayi sannan ya juya yaje wajen baffa Usman yabashi hannu suka kashe don shine gaisuwar tasu yana fad'in "Ina wuni baffanmu?."

"Lafiya klw malan bashar, za'a makarantar ko?"

"Eh.."

"To madallah, Allah yabada ilimi mai albarka."

"Amin." Yaron yafad'a tare da juyawa wajen baba balarabe daya hangosu asiya duqe agabansa suna gaishesa shima yaje yamiqa masa hannu sukayi sallama sannan ya gaishesa, dariya sosai yabawa baba balarabe ganin yanda yamiqo masa hannu suka gaisa batare da tsoro ba kamar yanda sauran yara keyi, yace

"Agaida yayana aminin baffansa, ALLAH yayi maku albarka." Ya amsa da amin mungode sannan yabi bayan 'yan uwansa da suka nufi cikin gida yana tsalle tsalle.

"Aminina kenan!, ALLAH yasa kagado mai sunanka da dukkanin nagartarsa."

Su baffa Usman suka amsa da Amin,  aranar baba balarabe yaga irin tsantsar soyayyar da baffa keyiwa d'an uwansa don gaba d'aya firar tasa komawa tayi akan rayuwar da sukayi da abokin nasa alokacin da yake raye, wani wuri yana basu labari yana dariya wani wuri Kuma saidai ya girgiza kai ya goge qwalla had'e da cewa ALLAH yajiqansa.

SANNU SANNU Bata Hana zuwa..Where stories live. Discover now