12

163 20 0
                                    

*TSAKA MAI WUYA.*

*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabooks:JamilaUmarjanafty*

https://chat.whatsapp.com/CPRnRPcAD5K8vEY91Ziz8V

Slm ina maiso taga tayi kiba jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga nono yacika yayi kyau ina maiso taga duwawu yafito kinzama cikakiyar mace ❤️ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku *ZUMAR K'IBA*, zumace wadda take saka k'iba cikin kwana 7 da yardar Allah *ZUMAR K'IBA*  zumace mai inganchi wadda aka had'ata da magun-gunan gargajiya Masu kyau da da tasiri ajikin d'an Adam,hajiya indai kina fama da rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kika sha zuma sai kin chanza..,Ina masu fama da  Ciwan sanyi  duk nacin sanyin ki hajiya kikai amfanin da maganin Mmn khairat saikin warke duk ko iya da d'ewarshi ajikinki..Domin k'arin bayani👉 WhatsApp no 07044450136, 08167453086

*12*

Haka kurum na ji na kwana da zumud'in tafiyar mu tarewar Adda Rukayya.
Abunda bai cika Damuna ba kenan wato shiga Mutane, shiyasa ko D'anwake ranar asabar d'in ban yi ba nace ma Amma zamu huta.
Amma tace daman ai ni ce ba na son jikina ya Huta ammh tuni tace na rika Hutawa ko sau d'aya a sati.
Tun safe na yi wanka na shirya Tunda Habiba tun jiya ta tafi, sai da na tsaya na yi ma Amma abinci na gyara daki wanka ne kada'i ba tayi ba tace min jikinta sai a hankali bazata iya wankan nan ba kila sai zuwa gobe.
Sai na Rabu da ita kawai daman mun yi da Ramatu zan biya mata mu wuce tare.

Inna talatu kuma tare zasu tafi da Adda Fati da zata biyo ta nan gidan su wuce. ina gidan kafin na wuce Suka iso gabad'ayansu da na so ma mu tafi tare sai nace ma Ramatu mu had'u achan kawai sai kuma na sauya Ra'ayi jin su Maman Salihi sun buga tsalle sun ce zasu je ma Adda Murna.
Ban san a ina ma suka ji labarin ba Kawai sai na ce musu sai sun zo.
Kayana na saka wanda Ramatu ta yi mana ranar sunan Noor. Sai na yi amfani da Farin Hijabina sabo ne lokacin Bikina da Salisu na d'inkashi.
Na saka takalmina mai saukakken Tudu tunda ina da tsawo ba na jin Dadin saka takalma masu Tudu.
Sai ga shi na yi yar kwalliyata har da Shafa hoda da kwalliya tare da man lebe Amma da su Adda suna ta fad'in na yi kyau da na kalli madubi sai da na yi dariyan kaina Fuskarta yar Sirit ce gaskiyan mgana komai na jikina karami ne ba Babba ba, hatta ko da kaina duk da tarin gashin da na ke da shi kana kallona zaka san ina da karamin kai. sai dai fuskar ta yi fasali Farar Hoda na saka daman ita nake shafawa,tunda ga yanayin Fatar Jikina ina da Haske sosai kamar wata zabiya.
Adda Fati na ta yi min d'an bikin na jirasu nace Wlh bazan tsaya jiran wannan gayyar tafiyar na su ba. Na ko yi tafiyata bayan na yi ma Amma sallama tace a dawo lafiya.
Na riga na yi yak'i da kaddarata shiyasa na yi Gundunbalan fita ba Abun rufe Fuskaa duk da ba wanda ya tareni da wata mgana ammh na sha nu ni da baki da Hannu ana zud'ena.
Adaidaita na samu zuwa pizzet daganan na samu na D'anmagaji tunda yanzu ta cikin Titin Tukur Tukur suke bi.

Karfe sha d'aya da wani abu na isa gidan Ramatu na iske Nura na gidan ashe ya dawo yana gari.
Na ganshi sai fama ya ke da Noor itama kuma Ramatu na ciki ta na Shiryawa. Shigowata na karb'eshi ina Fadin"Kawata muguwa ce. Shikenan sai ta barka da reno kai da ka dawo ka na Bukatar Hutu."
Yana dariya yace"Yauwa Hasiya ki yi mata Fad'a bata Tausayamin da na dawo kamar ta samu D'an reno"
Ramatu na daki ta daga Murya ta na Fad'in"In baka nan zan rena ammh fa in ka dawo kaima zaka Tab'a"
Kai ya girgiza kafin yace"Kin ji ta ko?
Ina sabata saman kafad'ata nace"Kyaleta da ni, zan yi maka mganinta."
Ramatu ta fito cikin Shirin Fita ta wurgamin zanin goyo tana Fad'in"Goya yarki mu tafi mun yi rana."
Ba musu ko na goyata Nura kuma ya shige ciki Ramatu ta bi bayansa sai chan suka fito tare.
Tunda yana nan shi ta bar ma gidan Ammh har bakin Titi ya rakomu muka samu abun hawa zuwa gaskiya Bayan Ramatu ta kira Adda Rukayya ta yi ma mai adaidaita kwatance wajen.
Cikin Lokaci ko sai gamu a sababbin anguwannin Gaskiya ne gida mai suna gida Baban su Amna ya gina Tunda babba ne a ma'aikatan MBAIS.
ko da muka isa mun iske gida cike da yan'uwa kamar ana wani Biki Adda Rukayya daga ita sai Habiba ne sai makotanta inda suka taso.
Gidan Babba ne shashen Adda Rukayya dakuna Hudu ne kowanne da Bayuka sannan ga Falo ga kitchen. shashen mai gidan ma babban waje ne sai kuma wani bangare da ba'a gama ba.
Tunda muka shigo na lura da yanayin yan'uwan Mijin sai faman nuna ni suke yi ana kus kus. Wanda ma bai sanni ba duk an gayamasa komai a kaina ban maida kai ba muka wuce cikin Dakin da Adda Rukayya take.
Abun mamaki ta yi maraba damu sosai ta saka wani leshi sabo ta ci kunshi da kitso kamar wata Amarya.
Kai tsaye ta kalleni tace"Hasiya sai yanzu.? Ba fa kowa sai ni kad'ai Allah yasa ma Habiba na nan"
Mirmishi kawai na yi ban ce mata komai ina ta kallon wajen gadajen duk Sabbi ne falon ne bakomai Kila ba'a kawo kayan ba ne. kafin ma mu tambayeta ta shiga gayamana masu kujrun ne ba su kawo ba sai an juma Gadaje kawai aka kawo sai kayan kitchen data siya tunda munzo muje mu tayata jera komai.
Hijabina na cire ban sauke Noor ba Duk da tayi barci yanzu ina Sauketa zata Farka. Habiba sai faman mopping din Tayels ta ke yi ta gama wankin bayi wai a hakama sun Rage ayyukan tunda tun jiya da Daddare duka dawo nan suka kwana.
Dangin mijinta kuwa suna tsakar gida ba abunda suke yi sai shewa da Hira.
Tare da Adda Rukayya da makotanta muka gyara mata kitchen d'inta wasu kayan duk Sabbi ta siya muna ji suna hira da makociyarta adashen dubu Dari Biyu ta shiga aka bata kwasan farko.
Kallona ta yi kafin tace"Hasiya na ware muku wasu kaya suna chan gidan. Har da wasu kayan amfani na cikin gida in Habiba zata dawo zata Taho muku da shi."
Kai na jinjina kafin nace"Mungode Adda Congrat Allah ya sanya alheri yasa an yi ma rai ne."
Ta amsa da Ameen cikin Fara'a kafin tace"Ina Adda Fati ne wai?
Kai tsaye nace"Suna tafe sai da ta biya ta gida ita da Inna Talatu da mutan gidanmu ne su Maman boy."
Adda Rukayya tace"Munafukai za'a zo ganin kwaf."
Ramatu tace"Su zo ai arziki ne sai su dagwala su kara gaba"
Adda Rukayya cikin Farinciki ta saka Shewa suka kashe da Ramatu ta na Fadin"Wlh kuwa su zo su sha kallo."
Nan suka cigaba da Hirar su da Ramatu tare da makotanta ni nawa kawai Mirmishi da eh ko a'a.
Babu wani sakin jiki ko shakuwa Tsakanina da Adda Rukayya yau ma na Fahimci tana cikin Tsananin Farinciki ne shiyasa.

TSAKA MAI WUYA.!Where stories live. Discover now