4

210 25 1
                                    

*TSAKA MAI WUYA.*

*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

Albishirinku ya yan'uwana An-Nisa! Ina wacce ta dade tana amfani da Sabaya amma bata ganin aikinsa duk kuwa irin shan da take masa ? To share hawayenki tamu Sabayar ingantacce ne wanda muka sake bakin aljihu muka zuzzuba kayan gyaran jiki wanda bana cutarwa ba infact shi wannan hadin 2 in 1 ne…. Hadin SABAAYA da ADUMULMULA, in kina fama da matsalar zubewar Nono to wannan had'i naki ne, in kinaso ki cicciko fatarki tayi kyau ki koma tamkar ‘yar yarinya to ki riki wannan hadi namu… Aikinsa bai tsaya iya nan ba hatta da kara lafiyar garkuwar jiki yanayi da kuma kara ni'ima…kowa na iya shansa, matan aure, Masu shayarwa in kin kusa yaye, 'yan mata, babba da yaro, maza da mata kowa na iya amfani da wannan hadi namu…. Muna maraba da mai siyan daya ko sari.

Abangare guda kuma muna had'a magani ingantacce na ciwon sanyi da yaki jin magani, in aka daure ana amfani dashi ana dacewa bi'izinillahi ta'ala, kai hatta da maganin hawan jini da diabetes duk muna saidawa kuma ana dacewa in sha Allah.

Atuntubemu tanan whatsApp or call 📞 07065481260..  Don Allah don annabi in kin san ba siya zakiyi ba kar kizo ki bata mana lokaci da tambayoyi please kayayyakinmu original 💯ne babu algus

*04*

*Bayan Sati D'aya*

Bayan Sati d'aya da sakin da Salisu ya aiko min da shi, Kamar ba'ayi ba. labarina tsakanina da Salisu ya Shud'e kamar bamu taba Had'uwa ba, Kayana da aka riga aka jera tun kwana biyu da sakin su Adda fati suka je suka kwaso min kayana. Maganganu da mugayen bala'i ba irin wanda Sahura da danginta ba su jefani da shi ba.
Wannan karon ma Dilalliya aka bawa ajiyan kayan sauran kuma Adda Fati ta tafi da su gidanta. Sauran kayan kitchen kuma gidan Ramatu na kai mata ajiya,tunda ita kad'ai ne a gidan kuma 2bedroom gareta, guda daya ne ke da gado d'ayan tarkace ne aciki.
Ko sau d'aya ban bari damuwar da na ke ciki ta bayyana saman Fuskata ba.
Saboda Amma nasan irin ciwonta nasan irin tashin hankalin da na ke shiga in Amma na ciwonta, shiyasa na ne kafa kafa da lafiyarta.
Ni kaina nasan na yi dauriya sosai ban zauna nayi kuka ba, ko hakurin Adda Fati da Ramatu suka rika ba ni, ko a fuskata ba su ga alamun na damu ba.
Duk da mgana ta zaga gari har gida ake zuwa da sunan yi ma Amma jaje, saboda kawai a ganni a fita ana nuna ni, a dangin Babanmu Baaba ce kad'ai ta lagos ta kira Adda fati suka yi mgana. Tace Goggon Kona ta fad'a mata aurena ya sake mutuwa, Kuma ta saka bayan Adda Fatin ta zo gida ta mata Flashing ta kira suka yi mgana da Amma.
Nima an bani tayi ta ba ni baki, Sai Baba Saminu da ya zo da safe Ana sati da abun ya share kafa yana ce ma Amma abun nan fa ya yi yawa,ya kamata a nema min mganin Farar kafa har da na maita ma.
Amma kamar ta yi kuka cikin Dauriya tace"Hasiya ba ta da Farar kafa, sannan ba ta da maita. Ba ta gaje ta ba, ni ba mayya ba ce sannan uban ta ma da Maye ne da kun sani"
Kalaman Amma yasa ya fara kame kamen mganganu kafin ya yi mata sallama ya shura takalmansa ya fice. Ranar Amma ta sha kuka, ni kaina mganar tasa ta dakeni Maita fa? Zargin maita ai abu ne mai wahalan sha'ani.
Saboda damuwar da na ga Amma ta shiga yasa na ce mata mu koma ga sana'armu tunda dai komai ya wuce, Da ya ke jarin duk ya lalace saboda sha'anin bikin nan, sai muka fara da Danwake ,shinkafa da waken sai zuwa gaba in jarin ya tarfu sauran siyayyan rogo da dawan ma Habiba taje kasuwa ta siyo komai ni ba ni da Damar Fita, Tunda in dai na fita sai na zama abun Nuniya.
Ni na ke jefa Danwaken Amma na taikamin da zubawa, kuma ana ciniki sosai, Saboda matan gidanmu suna siyan ma ya'yan su har da mazajen su. 
Da kuma makota tunda a irin gidajen da muke zaune ba kasafai akan Dora abinci ba yawanci an fi siyan irin su Danwake da Shinkafa da wake na Saidawa sai su awara a samu a ci a sha ruwa.
Duk da ina nuna komai ba komai ba ne ni kada'i nasan Halin da na ke kwana ina tashi, Kirjina suya ya ke yi ji na nake yi kamar ba ni da Sauran amfani,ammh in na Tuna Amma sai naga ina da amfani a wajen Amma bayan ni bata da kowa.
Salisu na raina, ba ni da in da zan samu labarinsa shiyasa na ke masa addu'an Allah ya bashi lafiya ya dawo da kafafunsa cikin koshin lafiya.
Habiba sai asabar da Lahadi take zama a gidan ranakun Sati kuma tana zuwa makarantar Boko da Safe, da yammah kuma taje islamiya, da Daddare kuma ta je makarantar Dare.
Shiyasa yawancin ayyukan gidan suna kaina, Daman kula da Amma ni na Daukeshi a wuyana da kaina ina Kafa kafa da lafiyarta fiye da tawa lafiyar.
Adda Rukayya sai sati uku da Faruwar abun ta zo gida tana ta yamutse yamutsen Fuska tazo ta sameni ina Dafa shinkafar yammah, tunda mun fara satin da ya shige lokacin da ta shigo ina kofar Dakin Amma ina gyaran shinkafa.
Sama da kasa ta kalleni ba ta tankani ba sai ni ce na yi mata mirmishi ina fadin"Adda Rukayya ke ce tafe?Sannu da zuwa."
A saman lebe ta amsani ta rab'ani ta shige ciki ina jinta Suna gaisawa da Amma. Shuru na dan wani lokaci kafin naji ta ta na fad'in"Amma ya mganr da muka yi? Tunda Fati ta fad'amin Shima Salisun ya saki Hasiyar"
Kai Tsaye Amma tace"Wata mgana kenan?
Yaya Rukayya tace"Mganar tafiyar Hasiya wajen Adda Hari mana. Amma shawarar nan ita ce Mafita haka ma Baban su Amna ya ce da na Fad'a masa."

TSAKA MAI WUYA.!Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon