*YAR FARI*
*بسم الله الرحمن الرحيم**HASKE WRITTERS ASSOCIATION*
Written by
'''zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on wattpad@zeeyybawa
#facebook@zaynab bawa novels
#IG@Zyernab Alabura'''*بسم الله الذي لا يضر مع اسمه شيء في الأرض ولا في السماء وهو السميع العليم."*
Page 11Iya tashin hankali hajiya tashiga tashin hankali awannan ranar, addu'a kawai takeyii aranta tana Allah yafito da safiyya lpy, kusan 3hour's aka d'auka cikin thratre d'in, nurses da sauran doctors d'inne suka fara fitowa, yayinda shikuwa abban abdoul yana ciki dawasu sauran nuraes d'in basu fitoba duk hankalin hajiya yayi wajan batasan wani hali safiyya take ciki hakaba dahar ynzu bai fitoba, sai bayan kusan 2hours sannan wasu nurses guda biyu suka bud'e qofa, fitowa sukayi sunajan patient bed dauke da ummin abdoul akai, babu wani alamun numfashi attare da ita, sai lokacin abban abdoul yabiyosu abaya yana qoqarin cire hand globe na hannunshi, hajiya tanufeshi hankali tashe tana jero masa tambaya, sadik yayane?" yanaga anfito da itabatako numfashii plz kada kacemun safiyya kwana ya qare, murmushi yayi wanda baikai har cikin zuciyarsa ba, dan ga alamun damuwa nan kwance akan fuskarsa, ya girgiza kai yace" hajiya anyi threatre Successifull sannan safiyya tananan lapiya kawai bata farfad'o bane dan anyi amfani da maganii mai qaarfii lokacin ana buk'atar bacewar hankalinta, Alhmdllhy alhmdllhy, hajiya take fad'i sannan taqara kallon abban abduol tana fad'in, sadik me'akacire mata, sanda yayi d'an jimm kafainnan yace" yara biyu duka maza amma kuma d'aya ya koma, amma d'ayan yananan cikin k'oshin lapiya, Allah yajikansa hajiya ta furta sannan tace" shikuma d'ayan Allah yarashi tafarkin tsira, amin jamillu ya amsa, sannan tace ina yaran suke?" yazo da raine ayi masa wanka da sallah akaishii, d'aga kai yayi yace, ehh dafarko harkuka yayi saidaga baya yacika, yasha ruwa acikine sosai, tsayawa hajiya tayi tana jimamii daga ganii wannan mutuwar yaron ta doketa, Danhar tafii abban abdul nuna damuwarta shikuwa yayi tawakalli ya miqa komai ga Allah, hakanma yana godiya ga Allah dayasa akayi akagama matarshi tana lpy, kuma ga yaro d'aya yabarmasa toh Alhamdulillah."
Hajiya ce! tazauna da safiyyya yayinda abban abdul yayiwa yaran duka hud'uba,(nasan mafii yawancinku zasuce tayaya za'ayi kuma bayan ya mutu ayimasa huduba, malamai dayawa sunyii magana kancewa har indai yaro yazo daraii, kafinnan ya mutu yoh yanada kyau arad'a masa suna yatafii kabarinsa dashii, walllahu ta'ala a'alam Allah yasa mudace sannan kuma Allah yasa muyi kykkyawan qarshe, amin) sannan aka shiryashi akakaishii, lokacii guda wannan haihuwar tazagaya ko'ina, yayinda akayita zuwa dubanta lokacin itakanma bata farfad'oba lokacin duk wanda yazo ba'abarii yashiga."Abdoul da baby sis tun ahanya driver ke sanardasu cewa umminsu ta haihu, zokaga murna wajan baby sis, ko abdoul dabaida fara'a sosai amma alamun jin dad'i ya bayyyana afuskarsa, duban driver d'in yayi sannan yace" Amma yajikin ummin nawa yake" Wangale baki driver yayi yana dariya yace" abdul babban mutum kenen gabaki d'aya hankalinka da tunaninka yafii namasu shekarunka yawa, abdul baice komaiba saikara maimaita tambayarsa dayayi nacewa" toh yajikinnata?" nidai banjeba mlm abdul amma najii ana fad'in jikinta alhamdulillah kuma y'an biyu tahaifa, amma D'ayan ya koma' Allah yajikansa abdul yafurta sannan yakara cewa kabii damu ta asibitin inason naganta, juyowa drivern yayi yana kallonsa kafinannan yace" abbanku yace nawuce daku cikin gida kuhuta tukunna shida kansa zaizo yad'aukeku yakaiku, shiru abdul yayi yajingina kansa jikin kujera batareda yaqara cewa komaiba, itakuwa baby sis banda tsalle-tsalle babu abunda takeyii na murnan anhaifo mata k'anii, cikin gida ya ajiyesu wajan umman asiya, anan suka zauna dan hajiya batanan tana asibiti."
Sai cikin dare kafinnan safiyya ta farfad'o, Alhmadulillah tafarko cikin hankalinta dake abban abdul yana wajan tana farakawa yafara dubata bbu wani matsala tattareda ita, dubanta yayi yace" Safiyya akwai wajanda keyi mki ciwone girgiza kai tayi ahankali kuma tafurta A'a saikuma tanuna wajan threatre d'in akan yanayii mata ciwo, Alhmdllh abban abdul ya furta sannan yace" wannan babu matsala normal ne, kaman dole saikinjishi ne, sai ahankalii, hajiyane tamatso kusada ita tana fad'in sannu safiyya Allah ya baki lapiya, motsa bakinta tayi tace" amin d'an dube-dube tafarayii abban abdoul yace mekike nema?" dawoda kallonta gareshi tayi sannan tace" ina abdul da baby suke?" suna gida hajiya tabata amsa, Tana maganane dakyar da alamu wajan threatre d'in nad'an damunta, dakyar tace" hajiya baby zatayi kuka akawosu nan, kallon abban abdul hajiya tayi tace" sadik kaje gida kad'auko mata yaran, zaiyii magana hajiya tayi saurin katseshi tace kajee kawaii, juyawa yayi yafita, office d'insa yashiga akan desk yasamu keys d'insa, shikam baimayi zaton zaigansu wajanba dan baisan yanda ya yasarba, hala wasu daga cikin ma'aikatansa ne suka d'auko suka ajiye masa akan desk d'in, qarasawa yayi yad'auki keys d'in, sannan yafito wajan parking na staff yashiga motan yanufii gida."
YOU ARE READING
Y'AR FARI
Historical Fictiona shekarun baya shekaru dari da hamsin da suka shud'e150yrs back anyi wata sarauniya mai suna asma'u yayinda tazo musu da sauyi na ban mamaki, bayan rasata sun shiga damuwa sosai, amma bayan shekara d'ari da hamsin aka kara haifo wata asma'un wanda...