Wa nake so? 47-48

330 28 3
                                    

*WA NAKE SO?* 💝💝💝
  47-48

WRITTING BY MARYAM S INDABAWA
MANS

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS*
(HAJOW)
✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Facebook @Maryam Sulaiman
Instagram @Maryam S Indabawa
Wattpad @MSindabawa
Email @Maryamsuleiman220@gmail.com

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI.

Dedicated to my lovelly sis *Nusaiba Suleiman Indabawa*

🌐🌐🌐 *_HAJOW HOT 10_* 🌐🌐🌐

❣ *_Wa nake so.?_*
_Maryam S Indabawa_ 💖
❣ *_Burin zuciya_*
_Bintu Shaik_ 💖
❣ _*Afreen ko Afra*_
_Princess Mayyat_ 💖
❣ _*Waye Angon.?*_
_Barrister Sady_ 💖
❣ *_Koshin Wahala_*
_Zeebusafana_ 💖
❣ *_Hakan Ya Cancanta_*
_Amyrad MD_ 💖
❣ *_Tsaiko_*
_Maman Sadeeq_ 💖
❣ _*Deezai*_
_princess Ameeroory_ 💖
❣ *_Nur~Al~Hayat_*
_Jidda ja'o_ 💖
❣ *_Tafi Jinina_*
_Nabiha Aminu_ 💖

_________________________

*** ***** ***
Abin mamaki kwana daya kwana biyu kwana uku dukka ba Kiran wayar Fu'ad kullum Zan Kira Amman a kashe abin fa ya Dagan hankali Dan Momy ma sai da ta gane.

Ina zaune a falo na sanye da wani sea green less wanda akai masa a do da brown and yellow. Dinkin riga da siket ne ba dan kwalli akai na sai gashi na da na faka yake kwance har a baya na. Ban yi kwalliya ba daga mai sai hoda da kwalli da na saka wanda ya kara fito min da kyau idanu na kuma sauka kara girma. Gashin ido na yai gazar gazar sai kace na saka gashin ido ko mascara. Baki na kuwa man lebe na saka sai kyalli yake. Daga kallo daya zaka gane ina cikin damuwa domin kuwa na zuba tagumi na lula can duniyar tunani. Har Momy ta shigo dakin ta gama kallo na ban sani ba. Wannan yasa tazo ta zauna a gefe na  tana fadin
"kwana biyu na rasa meke damun ki kina yawan shiga damuwa!"

Hawaye ne ya zubo min Dan me neman kuka ne aka jefe shi da kashin tumaki.

"To menene na kuka daga tambaya?"
Jikin Momy na fada ina fadin
"Momy yau kwana uku kenan bamuyi waya da Fu'ad ba kullum na Kira wayar a kashe!"

"Fada kuka Yi ne?"
Momy ta tambaya.

Kai na girgiza nace
"A'ah Momy tin Ranar dinner mu fa."

Kallo na Momy tayi sai tace
"Ki kwantar da hankalin ki Yana lafiya kinji."
"Momy na kasa yadda da hakan na kada cire tunanin hakan domin kuwa ba mu taba irin wannan jimawar bamu yi waya ba. tunani na Yana bani ko bai da lafiya. Momy dan Allah kije kuga ko lafiya Kinga Sani baya gari "

"To naji zani Amman ki daina kuka sannan ki taso muje falo gasu Fauwaz can sunzo."
Momy ta fada tana mikewa.

Naji dadin zuwan nashi Dan shi ke deben kewa Dan haka na Mike ina goge hawaye muka fito.

Ina fitowa na tadda Yaa Fauwaz zaune akan kujera sanye da black wando da blue black din riga mai long sleeve. Yai kyau idon sa makale da glass. Ina karasowa falon mu yai dai dai da Aiko yaron gidan.
Sallama yayi muka amsa sannan ya kalli Momy yace
"Alhaji Fu'ad ne yazo yace a fadawa Anty Fateema yana waje."

Ban tsaya Bata lokacin ba ko jin me Momy zata fada ba kawai na fice da sauri na. Daga Momy har Yaa Fauwaz da ido suka bini.

Ina fita naga motar sa a bude wannan yasa nasan yana cikin mota. Wajen motar na karasa na same shi zaube a cikin motar sanye cikin blue black din yadi yai Masa kyau. Sai tashin Kamshi yake.

kallo daya zakai Masa ka gane ya rame sosai. Kallon sa nayi da fuskar tausayi Ido na yana kawo ruwa,
"Ina ka shiga? Ina ka tafi ka bar ni?"

Na fada ina fadawa jikin sa tare da fashewa da kuka. Rumgume ni yayi Yana sauke ajiyar zuciya yana Kara Jin Sona da kauna ta na Kara shigar sa.

WA NAKE SO?Donde viven las historias. Descúbrelo ahora