Wa nake so? 77-78

362 24 0
                                    

*WA NAKE SO?* 💝💝💝
77-78

WRITTING BY MARYAM S INDABAWA
MANS

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS*
(HAJOW)
✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Facebook @Maryam Sulaiman
Instagram @Maryam S Indabawa
Wattpad @MSindabawa
Email @Maryamsuleiman220@gmail.com

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI.

Dedicated to my lovelly sis *Nusaiba Suleiman Indabawa*
🌐🌐🌐 *_HAJOW HOT 10_* 🌐🌐🌐

❣ *_Wa nake so.?_*
_Maryam S Indabawa_ 💖
❣ *_Burin zuciya_*
_Bintu Shaik_ 💖
❣ _*Afreen ko Afra*_
_Princess Mayyat_ 💖
❣ _*Waye Angon.?*_
_Barrister Sady_ 💖
❣ *_Koshin Wahala_*
_Zeebusafana_ 💖
❣ *_Hakan Ya Cancanta_*
_Amyrad MD_ 💖
❣ *_Tsaiko_*
_Maman Sadeeq_ 💖
❣ _*Deezai*_
_princess Ameeroory_ 💖
❣ *_Nur~Al~Hayat_*
_Jidda ja'o_ 💖
❣ *_Tafi Jinina_*
_Nabiha Aminu_ 💖

_________________________

*
Washe gari da safe Momy kadai ce ta yi aikin abin kari ta gama ta gyara gidan ta hade shi da turaren wuta. Yasmeen ta tasa tai wanka ta shirya sannan tasa ta zo ta tashe ni.

Da Sallama ta shigo dakin Gani na tayi kwance akan gado wannan yasa ta kira sunana
"Anty! Anty!!"

Jin ban amsa ba yasa ta fita. Momy tace
"Ta tashi?"
Kai Yasmeen ta girgiza tace
"A'ah bacci take!"

"Zauna ki karya ki wuce kada ki makara."
Nan ta hada tea ta nufi dakin Baba Uwani. Tana zaune akan sallaya tin asuba bata tashi ba. Zama tayi tana fadin
"Baba ina kwana?"

"lafiya lou. Kin tashi lpy?"
"Alhamdulilah! A kawo miki abincin nan ne?"

"A'ah barshi yanzu zan fito so nake nayi walha gaba daya sai na fito. Ina Fateema ne?"
"Yau bacci take yi bata tashi ba"

Momy ta mike ta fita tana kara gyagyara gidan. Karfe goma Baba Uwani ta fito sannan ta karya.

Abin ya basu mamaki domin har sha biyu ban fito ba. Momy tace
"Bari naje dai naga wane irin Bacci haka yau Fateema take haba har sha biyu."

Baba Uwani tace
"Ai na fada miki kila ba ita kadai bace."

"Uhmm!"
Kadai Momy ta fada tayo daki na. A kife ta sameni akan gado wannan yasa ta karaso da sauri tana fadin
"Fateema lafiya kuwa?"

Jin shiru yasa ta girgiza ni sai a lokacin ta lura da kamar bana numfashi. Cikin tashin hankali Momy ta hau kiran suna na tana saka hannun ta a kofofin hanci na. Tare da girgixa ni. A kideme ta fice a dakin tayi hanyar waje.

Baba Uwani na ganin ta fita ta mike tana fadin
"Lafiya?"

Momy bama tasan tana yi ba ta fice dan kira driver. Tana fita ta ci karo da Yaa Kamal zai shigo wannan yasa tai saurin kamo hannun sa tana fadin
"Zo ka gane min Fateema kamar bata da rai."

Haka tai ta jan hannun sa har dakin da Fateema take kwance. Baba Uwani suka gani a kai na tana shafa min ruwa a fuska amman sam ko gezau ban ba. Yaa Kamal bai tsaya wata wata ba kawai ya dauke ni. Momy da Baba Uwani suka biyo bayan mu. A mota ya saka ni muka wuce asibiti emergency.

Muna zuwa aka amshe ni suka shige daki dani. Momy na zarya hawaye na zubowa a idon ta addu'a take Allah ya tashi kafadu na kawai. Baba Uwani na zaune sai salati take tana fadin
"Jiya fa har sha daya muna zaune a falo muna ta hira sun cikan ciki da dariya ita da yar uwar amman jibi yau yadda muka dauke tankamar gawa. Kai Allah dai ya gajarta wahala. Yanzu in mutuwa ce ma shikenan. Inna illiahi eainna illahir Raji'un. Kai Allah dai ya tashi kafadun Fateema. Allah ka bata lafiya."

WA NAKE SO?Where stories live. Discover now