Wa nake so? 75-76

312 31 2
                                    

*WA NAKE SO?* 💝💝💝
75-76

WRITTING BY MARYAM S INDABAWA
MANS

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS*
(HAJOW)
✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Facebook @Maryam Sulaiman
Instagram @Maryam S Indabawa
Wattpad @MSindabawa
Email @Maryamsuleiman220@gmail.com

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI.

Dedicated to my lovelly sis *Nusaiba Suleiman Indabawa*
🌐🌐🌐 *_HAJOW HOT 10_* 🌐🌐🌐

❣ *_Wa nake so.?_*
_Maryam S Indabawa_ 💖
❣ *_Burin zuciya_*
_Bintu Shaik_ 💖
❣ _*Afreen ko Afra*_
_Princess Mayyat_ 💖
❣ _*Waye Angon.?*_
_Barrister Sady_ 💖
❣ *_Koshin Wahala_*
_Zeebusafana_ 💖
❣ *_Hakan Ya Cancanta_*
_Amyrad MD_ 💖
❣ *_Tsaiko_*
_Maman Sadeeq_ 💖
❣ _*Deezai*_
_princess Ameeroory_ 💖
❣ *_Nur~Al~Hayat_*
_Jidda ja'o_ 💖
❣ *_Tafi Jinina_*
_Nabiha Aminu_ 💖

_________________________
Budewa na fara kirji na na bugawa. Rubutun Fu'ad ne ya bayyana akai wanda yake mai kyau dashi kamar computer ce ta rubuta shi. Shafa rubutun nayi sai kuma na maida ido na kan farkon takardar.

"Assalamu alaikum ya ma'abociyar kyau nustuwa....."
Kofar dakin naji an budo wannan yasa na juyo. Yasmeen ce tsaye cikin shirin ta na makaranta.

"Ina kwana Anty?"
Murmushi na saki na mike nace
"Lafiya lou har kin fito?"

"Eh Momy tace ki fito mu karya."
Waya ta na dauka na bi bayan ta muka fice na bar takardar akan gado.

A falo na samu Baba Uwani na durkusa na gaishe ta ta amsa tana fadin
"Kin tashi lafiya?"

"Alhamdulilah."
Nan muka karasa dining muka karya. Muna gamawa Yasmeen ta mike ta fita driver ya tafi kai ta. Anan falo muka zauna muna hira dasu Baba Uwani har da Momy.

Har karfe sha biyu muna zaune. Bana minti goma ban kara trying number Fu'ad ba har Momy ta lura tace
"Lafiya dai ko?"

Fuska ta cike da damuwa nace
"Momy number Fu'ad ne bata shiga."

"Ke kuma da saka damuwa da fargaba ko? To ai kika sani ko ba charge ne ko aiki yai masa yawa shiyasa."
"But Momy tin ......"

"Please Fateema ki kwantar da hankalin ki yana lafiya kinji ko? Nasan zai kira ki da ya samu dama."
"Shikenan."

Na fada ina mikewa. Kallon Baba Uwani nayi nace
"Baba me zan dafa mana ne?"

"In abinda nake so ne wahala zaki sha,  gashi kuma kamar kina da yaron ciki."
Ido na zaro nace
"Kai Baba ni ba ni da komai."

Dariya Momy tayi tace
"Me kike so Baba?"

"Dambu nake sha'awa wallahi."
"Nima shi nake sha'awa."
Na fada.

Momy ce ta kallen tace
"Je ki daura dambun akwai barzaziyar shinkafa a store."

Kitchen na tafi ina murmushin maganar Baba wai ina da yaron ciki. dariya nayi nace
"Ni da ba abinda ya shiga tsakani na da Fu'ad din ma."

Baba tace
"Dan Allah Huwaila ba ciki ne da Fateema ba?"

"Me kika gani Baba?"
"Gani nayi tayi haske sai yar ramar da tayi shiyasa nake zaton hasken ciki ne da ramar."

"To wa ya sani ni dai bata fada min ba."
"To Allah ya inganta."

"Amin!"

*
Ina shiga kitchen na dauko barzaziyar shinkafar na wanke sannan na dauko tukunyar dambu. Wanke barzaziyar shinkafar nayi na zuba a cikin tukunyar dambun bayan na zuba ruwa a kasa na daura akan wuta.

WA NAKE SO?Where stories live. Discover now