WANI GARIN... yafi GABAN KUNU 30

261 18 0
                                    

🍚 *WANI GARIN*.........🍚






*HUMAIRAH B MELODY*




*Wannan shafin nakune group din MUSHA KARATU NA YBK Allah ya kara daukaka y as bar LOVE.*


             30

Salma na fitowa tayi wani gwauron numfashi ta zauna kan kujera ai da gudu tafice tana fitowa harabar wajen tadan sassauta cikin ranta cewa take "Allah kaike iya mana salatin annabi kawai takeyi akan Allah Ya taimaketa ta tsallake sharrin alhaji chile"
Tana isa gida bata tsaya bata lokaciba Jakarta kawai ta dauka tayi sallama da gida motarta ta dauka dayake kwararra ce wajen tuka mota gudu takeyi kaman zata tashi sama cikin awa biyu sai gata a Zaria sai kabama inda gidan ambil yake Don sun tashi a unguwan kaya, horn tayi mai gadi Ya bude HURUL'IN ce tafito ta rungume salma tace Auntina batada lafya dafatan kin kawo mata magani, SALMA ta ware ido tace HURUL'IN ai likita ke bada magani kuma uncle dinki tsohon likita ne meyasa bai bata magani ba?  HURUL'IN tace yace tayi hkr ciwonta baida magani sallama sukayi ambil kwance a three sitter cikin wani bankamemen falo  tana ganin salma ta Mike ta tarbeta suka zauna ambil tace "Ya Allah kabarmu Da masoyanmu ka tarwatsa makiyanmu salma ke jaruma ce dakowani namiji zaiyi shaawa you are such a darling Kinyi mun halacci Kuma bazan manta ba"
    Salma ta nisa tace gaskiya wannan aikin namu saida Raine mude muci gaba da kaiwa Allah kukanmu Don nasan bazai taba bamu kunya ba,
salma ina documents din Don sunake son gani salma Tamika mata salma naganin sunan mahaifinta ta fashe Da kuka tace "Ya Allah karka bar alhaji chile haka yatafi a free yayimun yankan kauna yarabani da iyayena lokacin danake tsantsar bukatansu Allah nagode maka daka dawomun da rabin farincikina saura daukan fansa Da kotu zata bani dama dana kashe alhaji chile Da hannuna kuka Takeyi mai tsuma zuciya Wanda Nikaina saida na tayata kuka saboda rashin iyaye babban ukuba ne cikin rayuwar mu Amman yaza tayi Daman tun ran gini tunran Zane, salma ta matsa tace Kiyi hkr Bakiyi rashi ba Amman Kinyi dacen miji daace zansamu kwarzo haxiki kamar mijinki da duniya tazamemun zuma dakuma bazan taba kukan maraici ba, nan sukayita hira ana saka wannan ana warwarewa har Ambil tasanarda salma cewa tana daukeda juna biyu inda tayi farinciki King sai dare yadawo dayake Yanzu yaxama Dan kasuwa tabbas yanajin dadin kawancen ambil Da salma.
KOTU
A kotun Sharia ta biyu dake GRA a GARIN Zaria Wanda akafi sani Da kotun cherdiya nan salma tasamu aiki a matsayinta babbar lauya bayan mutuwan Gali wazeeri tashiga office Da adu'oi tafara aiki gadan2 kowa son salma yakeyi saboda kowa tana Yanke masa hukunci daidai Da laifinsa wajen mata kuwa wayanda Maxa ke muzguna musu tana daukan mummunan mataki saboda babu abunda ta tsana taga Mace cikin kunci inta kama har yari takankai Mutum Don kwatowa Mace yanci, zama takira Wanda akafi sani Da meeting inda tasanar dasu case din dake hannunta sunkuma Goya mata baya Don Labarin ambil abun ayima toshiya ne, an rubuta takardar Sammaci zuwaga chile akaba messenger har garin Abuja inda yasameshi yamika masa sannan ya juyo.
      Alhaji chile yayi matukar mamaki Sammaci daga kotu?  Laifin meya aikata tuni yakira malaminsa yasanar dashi yayi istihara yakirashi yace "Asirinka yakusa tonuwa kuma bakada wani zabi illah halartan kotun Don ganin waye wannan me karar naka saimusan abunyi Don nakasa ganin komai saboda karfin adu'oi dasukayi akanmu, Kuma wata takusa dakai ce"
karaf alhaji chile ya kashe waya tafara tunani salma ce kawai tafado mishi Gashi bashida contact dinta basu shiga duka.
   Gida ya isa a area 11 garki yadda kowa yagansa hankali Ya tashi zagayeshi akayi Amman zufa kawai yakeyi yace "wata kotu na nemama ranan litinin kuma yaxama dole inje in amsa kiran kotu saboda rashin zuwa WANI laifi ne"
  Fadeela daya daga cikin yayansa Wacce itama Barista ce tace baba kafana kafanka bakada wani lauya daxaka dauka karbar komai a hannuna kuma koma meye zakasan cewa bakayi asaran haihuwana ba, cewa yayi ke dallah rufemun baki Yaushe kikazama lauya dazaki iya kareni lauyoyi Zan dauka irinsu BASHIR shuaibu miyagun Wanda Allah Ya isa bata musu komai Kiransa yayi sanar dashi komai ranan litinin suka halarci kotu.
ZARIA
jikake Mutane sun tashi suna cewa koooooootuuuuuuu saida SALMA ta zauna Da king da neehlah dasu hajiya suna baya sun zauna Gayan kallo harda ni HUMAIRAH danaci atampha Riga Da skirt 10pcs mai ruwa peach Da gyalena tokoise blue sanye da glass.
salma tagama rubuce rubuce tadago sukayi ido hudu Da chile tuni ta watsa mishi kallo itako ambil tana zaune wajen zaman lauyoyi karfin Hali kawai takeyi Amman yazama dole takare Kanta Da martabar iyayenta dasuka rigamu gidan gaskiya.
KOH WANDA AKE TUHUMA YANADA LAUYAN DAZAI KARESHI?
    BASHIR shuaibu yafito yace gani nine mai girma mai Sharia.
INA BUKATAN GANIN WANDA AKE TUHUMA A GABAN KOTU.
   saiga alhaji chile an tasoshi tareda yan sanda salma tabada umurnin akaranto laifin chile ai saida Ya rude, kotu taba ambil Daman yiwa alhaji chile tambayoyi fitowa tayi ta tsaya a wajen Kanta ta gaida mai girma mai Sharia ta gaida kotu tafadi sunanta saida alhaji chile ya raxana kannan tafara wurgo musu tambayoyi.
    *kozaka iya sanar Da kotu halakar dake tsakaninka Da alhaji Ibrahim LAWAL yabo?  Kafin kayi sanadiyyan kasheshi ka kashe yaransa bayan ya danka masa dukiyarsa?*
     Alhaji Ibrahim LAWAL yabo amininane Kuma shakikina Wanda muka Baro mhaifanmu zuwa GARIN Abuja Amman banida masaniya gameda mutuwarsa kuma zancen documents babu wannan maganar.
*Tunda kace bakada hannu aciki zaka iya ranan wata laraba dakuka tattauna dashi alhaji Ibrahim LAWAL yabo acikin lambun gidansa har bayan yaje dauko maka documents kakira wasu kukayi magana har yarsa ambil tayi maka magana kayi ikirarin Inhar tafadi saika yankata?*
   alhaji chile yaji zufa yace wannan maganar banzace.
Objection my lord tambayoyin sunyi tsauri.
salma tacema ambil a gyra salon magana,
*Inada bukatan amsa Don wannan tambayar Tanada matukar muhimmanci a garemu duka*
mezai Hana maigirma kotu ta watsar da wannan maganar saboda Wanda yariga yamutu Ya mutu.
*Alhaji idan ka kasa bani amsa inada mafita Wacce kotun mai girma zata duba* CD ambil takawo aka hada komai akasa maganar dasukayi da salma a office kowa yaji salati kawai akeyi salma tabuga guduma tace silence,
*Ambil tajuyo tace ya mai girma mai Sharia wannan kadai Ya isa sheda Kuma kotu tayi gaggawan Yanke masa hukunci* tayi Godiya ta zauna salma tayi rubuce rubuce tace koh lauya mai kare Wanda ake TUHUMA yanada abun cewa? Yace Eh yafito daka ganshi kasan makirine tuni Ga gaskiya Amman ya juya kotu ta dage ZAMAN wannan kotu zuwa 12-11-2017 Amman Da sharadin Kai Wanda ake TUHUMA gidan yari koh beli miliyan goma bsbu lamani.



muje zuwa mahaukaci yahau kura

HAPPY JUMUAT

WANI GARIN.....yafi gaban kunuDonde viven las historias. Descúbrelo ahora