fadimatuz zahra u

625 38 3
                                    

ZAHRA

Page 1
Bissimillahir rahamanir rahim

"Zahra amshi kudin nan maza kije kisiya min kati a shagon shamsu"_amsar kudin nayi ina kunku ni na nufi
waje ina jan kafa(takalmi ) "sharaff sharaff"kamar wata budurwar kauye(uhmm karfa kuyi tunanin nima a birni aa kawai muna birni ce lolz) ina fita kofar gida na walwala da wani uban gudu yadda Kasan naga wani katan dodo, bantsaya a ko ina ba sai a kofar shagon shamsu mai kati,ina zuwa na mika masa yakushashshiyar dari dake hannu na nace"shamsu aban kati" jiyuwa
yayi yana kallo na kamar mai nazarin wani abu kafin daga bisani yace"shamsu baya nan yatafi makaranta koyan sallama" "eh lalla wanna mutimin yama raina min hankali ,,,,,,,,,,toh kodai yan biyu ne "abun da nafada kenan a zuciyata a fili kuma cewa nayi " ashe dama ku yan biyu ?toh bani kudin idan shamsu yadawo na zo nasiya" dariya suka kwashe da ita jin abinda nafada, nikuwa na musu kori da ido ina kallanso ina tunanin to miye abun dariya anan, miko min kudin yayi yana kokarin hadiye dariyarsa yana cewa"toh gashi anjima idan yadawo sai kizo kisaya"
Karban kudin nayi najuya ina sauri domin naje gida na bawa mama labari domin nasan cewa batasan shamsu yan biyu bane ba, tundaga kofar gida nake kwala mata kira "maaaaa maaa maa na kinsan miye"
Mama dake zaune a tsakar gida rike da wayarta a hannunta tana jira in kawo mata kati tasaka ta amsa gameda tambayata mai ya faru "hmn mama ashe waidama shamsu yan biyu ne?"naci gaba da cewa"yanzu da naje siyo kati naga dayan shamsun kinga shi kuwa maama kamar su daya sak wlh da shamsu, wai saiyace min wai dayan shamsun yatafi makaranta koyon sallama"
"Mama ashe dama Shamus bai iya sallama ba? "Kuma fa............"
"Dallah yiwa mutane shiru marar wayu kawai kekan zahra sai dai ina miki addu'a Allah ya shiryeki da wauta yanzu dakika je din bakiyi sallama ba haka kawai kikaje kandan kandan kamar wata sukowa" mama tafada cikin fada nan take naji jikina yayi sanyi domin kullum idan nakawoma mama tadi saita gwale ni wata ranama har dukana take yi, wa sai tace wai kannena ma sunfi ni dabara uemm Allah sarki ni,(hhhh su zahra manya) tsawar da mama ta daka min ne yadawo dani daga tunanin dana lula, "kitashi kije ki siyomin katina yanzu yanzu nan idan bahaka wlh sai namiki dukan kawo wuka a gidan nan kuma saura kar kiyi sallamar idan kika je mama tafada
tana kawo mun duka, jiki bakwari na mike ina tafiya a hankali na nufi shagon shamsu
.............................................,.............,....................
Fateema Adamu Gamawa
Toh fa readers kuya zahra
zasu kaya da ita da mai kati

I dedicated this page to Mama Malama(Jamila Abubakar kd)

FOllOW COMMENT & VOTE THROUGH WATTPAD@ FateemaAdamu

Fateegamawah loves u fans

ZAHRAWhere stories live. Discover now