Chapter 1

626 46 3
                                    

*©®Hakkin mallaka nawa ne ni Khadeeja Candy, ban yarda a sarrafamin labari ta kowace siga ba balle har a dorashi a Website ko YouTube ba tare da izinina ba, yin hakan kuskure ne babba domin zai iya janyowa mutum matsala saboda haka a kiyaye ⚠*

SHIMFIDA...

“Ni ma ina da buri, ina da mafarkai irin na kowace mace, sai dai kuma kaddara ta shata min liyi, yadda alƙalamin ya zana dole haka zanbi...
Daga lokacin da na fahimci haka, sai tsoro da fargabar me zai faru a gaba ya fice a zuciyarta. Tafiyar da babu dawowa ta zama dakuna...”

TA ƘI ZAMAN AURE...
Share fagen wata tafiya ce mai sarkakiya da daure kai. Wata kalar kaddara ce mai rikitarwa, shimfida ce dake lalaye tafiyar wasu daidaikun mata....

Tafiya ce ta irin matan da duniya ta canja musu zane, suke da wani rufaffen sirri a zuciya! Sai dai kadan daga masu ilmi ke fahimta. A cikin rayuwa akwai mutuwa haka ma a cikin mutuwa akwai rayuwa shim kun ankara da haka?

Mabudin kowace kofa makulli ne sai dai wannan kofar a balleta ne ta kasa, sai shigar cikinta ta kasa yi ma mai dakin dadi.
Al'umma sun kasa yi mata uzuri iyayenta  sun kasa fahimta, mazajen kuma sun kasa riko...! Uba na gari jigo, sai dai ita bata dace ba, miji na gari gimshiki a nan din ma dai bata dace ba, kuma duka laifin yana komawa zuwa gareta ne.... Duniya ta yi mata juyin masa, ta yadda ta kasa banbance fari da baki, ji da gani sun mata nisa,  albishin daya take jira... mutuwa...!

Masoyana Assalamu Alaikum Khadeeja Candy ke muku sallama tare da fatan na same ku cikin aminci da kwanciyar hankali.
         Gani dauke da wani sabon labari kuma ina fatan zai kayatar da ku fiye da sauran. Labari ne akan NOOR da rayuwarta da iyalan gidanta.
Labarin nan kirkiren labari ne idan yayi daidai da rayuwar wasu ko wata to arashi aka samu. Za ku fi samunsa a AREWABOOKS @KhadeejaCandy

Ranakun posting. Monday - Friday

Chapter 1

بِسْمِ اللّٰهِ الرَّحْمٰنِ الرَّحِيْمِ

Tasss muka ji sautin saukar mari, irin marin da zai iya kurmantar da mutum a take. Na kai hannuna da sauri na dafe kuncina hawaye na sauko min. Hana ta rufe fuskarta ta fashe da kuka, kamar yadda Mama ma take kukan marin da Abbah yayi mata.

“Abun da na ga damar badawa kenan idan kin ga dama ki zubar daman baki taba godewa ba ai baki taba godewa ba idan na yi miki abu, kullum cikin kuka kike kuma a cikinsa zaki kare Hajara...”

Ba a iya fatar baki yake mata fadan ba, sai da ya hada mata da duka yana harbin kafafuwanta har sai da ta fadi. Da gudu na nufi gurin da take ina kuka, sai dai kamin na tabata sai ya fisge ni ya jefar a kasa.

“Abbah dan Allah ka yi hakuri”

Na fada ina kokarin tashi na sake nufa gurin da mahaifiyata take. A madadin yayi hakuri sai ya kara rufeta da dukan kamar ana kara masa karfi, ya saba idan ya fara dukanta sai ya canja mata kamannin sannan yake barinta, dukan mahaifiyarmu a gaban idonmu wani abu ne da Abbah ya saba yi, tun muna kanana har girmanmu, agaban kowa zai iya fada mata magana marar dadi, idan kuma ta yi masa ba daidai ba baya duban mu ko a tsakar gida zai iya rufe ta da duka, mu kuma muka kasa sabawa da halinsa. A kullum idan yana dukanta na kam ji kamar ni yake duka zubar hawayena suka fi nata yawa domin ko bayan abun ya laba na kam kebe na yi kukan abun da Abba yake mata.

“Dan Allah Abbah ka yi hakuri...”

Na sake fada ina kwantawa ta inda yake shurinta domin na tare mata, sai ya hada har da ni yana shurin har sai da yayi mai isarsa sannan ya kyale mu ya fice daga gidan. A nan na samu damar tashi na rika Mama ita ma ta tashi, da taimakon Hana  muka kaita daki, karfi hali irin na Mama muna shiga dakin sai ta yanke kuka da take ta share hawayena ta dubu mu ni da kanwata Hana ta ce.

TA ƘI ZAMAN AURE...Where stories live. Discover now