Chapter 11

139 21 2
                                    

Follow the KHADEEJA CANDY channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01

*Duk mai son ya rika samun Littafin TA KI ZAMAN AURE yayi following wannan Channel din mai suna KHADEEJA CANDY a nan zaku rika samu duka littafaina in Sha Allah*

✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧

𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆

*Talla👇👇👇*

https://chat.whatsapp.com/GY1W0qJiFbJD5A5J6F0fqA
*INA MATAN DA SUKASAN DARAJAR GYARA❓DAKU NAKE MACE MAI GYARAN BATA ZAMA BORA❌*

*KUZO GA INGANTATTUN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI💪BA MUNA KAYABA❌ HAJIYA KIZO KISAI KAYAN MATA WURIN DA BAZAKIYI ASARAR KUDIN KI BA*

*INA MASU CEWA NI KO NASHA KAYAN MATA BASAMIN AIKI HMMM HAJIYA BAKIDAI SIYA KAYA MASU INGANCI BANE, KAYANMU SUNA KARA NI'IMA, TAYARDA SHA'AWA, DADI, TIGHTENING (MATSI), CIKO DA GABAN MACE (DUK BUDEWAR SA), DUMIN GABA GA, KAMSHIN GABA GA KUMA NA KARA DANDANO OVER 💃💃💃💃💃👉 GA KUMA INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI DAGARGAZA SANYI KODA YA SHEKARA 10 A JIKINKI* 09038090328

*A DAYA BANGAREN KUMA MUNADA SABAYA MAI GYARAN NONO DUK LALACEWAR SA KO KIN HAIHU GOMA SABAYAR MU ZATA CIKO MAKI DA BREAST SUYI GIRMA SOSAI MADAME*

*GA KUMA TA HIPS (MAZAUNAI)SU CIKO SUYI BULBUL NONO YA CIKO SOSAI HJY KIYI KIBA YAR DAIDAI SKIN DINKI YAYI KYAU KI KOMA TAMKAR TARWADA*

AKWAI KUMA NA GYARAN NONO WANDA BAYA SAKA KIBA💃💃💃

GASKIYA NA YARDA DA INGANCIN KAYANTA👆👆👆


*Chapter - 11*

Ban bude ledar da na isa da ita gida ba, kudin ma sai na boye ban bari Mama ko Hana sun gani ba. Bayan na yi sallah La'asar Mama ta kira ni na fito ta ba ni danta malelen da aka girka, ko karba ban yi ba na ce na koshi daman wadda ya ci kayan dadi me zai yi da wani malele.

“Me kika ci?”

“Na ci abinci a can”

“Yanzu gaban maza kika zauna kika ci abinci saboda ki nuna ba ki da tarbiya? Kuma rokonsa kika yi? Ai na ga kin dawo da ledodi kin boye baki nunawa kowa ba. Yanzu duk abubuwan nan da suka faru kwana biyu ba su isa su zame miki darasi ba? Wai Noor idan baki yi hankali yanzu ba yaushe zaki yi hankali? Matukar baki canja rayuwa ba zaki sha wahala nan gaba, ki ce yayar Hannatu amman ke ce shashasha”

Na sauke kaina kasa ina jin kalamin na Mama yana min yawo a zuciya ta bangaren rashin dadi.

“Ba a gaban maza na ci ba, ni kadai ce lokacin da na ci, ya bar ni a dakin ne sai da na koshi sannan ya dawo”

Bata sake ce min komai ba, kuma daman bana wani abun fada dan haka na juya na koma dakin. Ban sake fitowa ba sai da aka yi sallah magariba ina gama sallah na kwanta ina jiran Yaya ya shigo na ari wayarsa na kira Zafeer domin na san Mama ba zata bar ni na fita na je gidansu Zainab na ari wayar Mamanta.
Bayan Sallah Isha'i Baba ya shigo gidan, ina jinsa na yi saurin dauko leda daya da na shigo da ita na dauko kudin da na boye na fito na tare shi.

“Baba sannu da zuwa”

“Yauwa”

Ya amsa min kamar yadda ya saba da daure fuska, na dan tsawon wuya na leka dakin Mama na ga bana hangota sannan na mika masa ledar hannuna.

“Gashi Zafeer yace a baka”

Na hada masa da kudin da na karbo gurin adashen Mama. Baba ya karba yana dubawa.

“Me ye ne”

“Ban sani ba ni ma cewa dai yayi a kawo maka”

Ya bude abincin da ya fara expire saboda yana cikin leda kuma gashi na masa mugun boyo. Sannan ya kirga kudin na yi zaton dadi Baba zai ji saboda ya min gori jiya cewar Zafeer be taba ba shi ko dubu goma ba, a tunanina hakan da na yi zai haifar da faeinciki da jindadi a zuciyar Baba sai na yi arba da tsabanin haka.

TA ƘI ZAMAN AURE...Where stories live. Discover now