Chapter -4

120 15 0
                                    

KAREEM POV.

After fitarsu, Yusura ta fito daga kitchen rike da cup din ruwa.

“Me za a girka anjima?”

Daf da zata wuce shi tambaya. Ba tare da ya kalleta ba ya amsa.

“Ba a gida zan ci abincin dare ba”

Ta daga kadunta alamar ko a jikinta sannan ya wuce ta haye sama.

Mike tsaye ya saka hannunsa daya a aljihu dayan kuma rike da wayarsa a hannu ya sake cewa daga falon ya nufi gurin da ya saba zama. Sai da ya isa gurin sannan ya amsa kira na biyu dake shigowa wayarsa.

“Hello”

“Darling na yi missing dinka badly”

“Toh ya muka iya, tun da mijinki ya ki barin gari? Sai hakuri”

“Zamu iya haduwa ko yana gari...”

Yayi murmushi ya shafa sajensa.

“aa kar dai mu shiga hakkinsa da yawa, kar zunubin ya mana yawa, kara idan baya gari wannan kina da Hujja”

“Wata kila baka yi marmarina yadda na yi marmarinka ba ko?”

“Na yi mana, amman dai kar mu wuce gona da iri, kin san ai yadda nake kaunarki”

“Ko kirana baka yi Kareem”

“Be kamata na kira ki idan mijinki yana gari ba, akwai abubuwan da na iyakancewa kaina aikatasu, Safeena dole muna hakuri da wani abun fa”

“Kawai dai baka so na kamar yadda nake son ka shiyasa”

Ya shafa kansa yayi murmushi.

“You're the love of my life, ke kadai kika na aikata wani aiki da zai ba ni zunubi mai yawa Safeena, ke kin sani idan bana sonki ba zan yarda wata mu'alama ta hada mu ba haka ne?”

“Eh amman...”

Sai kuma ta yi shiru kamar wadda ta rasa abin cewa.

“Yau na ga wata yarinya mai yanayi da ke, har ta fiki wauta da sakarci ma”

Yana maganar yana murmushi.

“A ina ka ganta?”

Ta tambaya daga dayan bangaren.

“Wani yarona na gurin aiki ne ya zo duba ni sai ta biyo shi, ina kallonta ke nake ta tunawa”

Shiru ne ya biyo baya har na tsawon lokaci.

“Safeena...”

Ya kira sunanta sai ta amsa masa da muryar dake nuna ta damu.

“No wait ba abun da kike tunani ba ne, ke kin cika kishi fa, ba yadda kike zato ba ne, babu wannan a zuciyata har abada ke kadai ce kwallin kwal...”

Ta sauke ajiyar zuciyata.

“Duk ranar da ka so wata Kareem zan iya mutuwa”

“Ba zaki mutu ba, saboda ba zan so ba, na san yadda kike da tsananin kishi ai, zan kiyaye”

“Ina fatan haka”

“Ina mijikinki yake?”

“Yana daki, ni kuma ina harabar gida ne”

“Ni ma ina harabar gidan, amman yanxu zan fita, je ki samu mijinki zamu yi magana anjima”

“Okay i love you”

“I love you too”

Ya sauke wayar yana murmushi. Kana ya busar da iskar bakinsa ya sake shafa kansa ya sauko zuwa sajensa. Sannan ya juyo ya fito daga garden din ya nufo cikin gidan. Ganin kofar falon bude ya fahimtar da shi bako ya shigo gidan, domin daga shi har matarshi da yaransa biyu basa barin kofa a bude. Be karasa ba ya ji sautin kuka da kara mai razanarwa da muryar da be tantance ba. Hakan ya kasa shi cira kafa ya shiga falon da sauri. Yarinyar da ta fita dazun ya gani tsaye kusa da kofar rike da kai tana ihu, Yusura na tsaye gabanta rike da glass cup.

TA ƘI ZAMAN AURE...Where stories live. Discover now