Chapter -3

180 20 4
                                    

https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx

Assalamu Alaikum...
Ina talata muku
KHADEEJA CANDY STORE 🥰🙌
Muna siyar da Atamfa, Laces, Mayafai, Talkami da Jaka, Akwaituna, Kayan Kitchen, Zanen Gado, da kuma kayan kawata gida ko falo.

✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧

𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆

𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫  -3

Ina zaune a gurin wasu iyalai suka shigo, ba zan iya fadar cewar masu kudi ne sosai ko akasin haka ba. Sai dai alama ta nuna suna da rufin asiri. Teburin sake gabana suka kama yan mata hudu ne sai maza uku da kuma magidancin da zan iya shaidar cewar mahaifinsu saboda kama da tsufan da yayi. Wadda ta zauna a gefensa kuma bana bukatar a fada min cewar ita din uwace domin alamu ya nuna haka. Hannu biyu na saka na yi tagumi ina kallon yadda uban yake handling yayansa mazan suka koma a dayan teburin suka zauna matan kuma suka zauna tare shi.

Sai da suka fara daukar littafin dake teburin suka duba kalar abincin da suke so, tukuna daya daga cikin ma'aikatan gurin ya zo yayi taking orders. Ni kam sai kallonsu nake cike da burge, ba kudin ne abun burgewa ba, ba zuwa restaurants ko order abinci, soyayyar ce ta shiga zuciyata yadda uba yake nunawa yayansa soyayya da kauna yana ta hira da matan suna dariya mazan kuma suna jefo na su hirar daga can inda suke zaune. Wani abu ne da ni na rasa tun tashina, ban tana zama da mahaifina ya tambaye damuwata ko dadi ba, wata hirar farincikin bata taba hada ni da shi ba, ban taba aikata wani abu ya nuna jindadinsa.

“Noor....”

Na juyo dama da ni sai na yi arba da Yayana, hannayensa na ji a fuskata yana share min hawayen da ban san sun zubo ba.

“Kuka kike yi? Saboda na dade?”

Ya tambaya saboda ya san ni da kukan shagwaba kamar wata wadda ta tashi cikin gata. Sai na girgiza masa kai na juya na kalli mutanen

“Wani abu da na rasa nake kallon wasu da suke da shi, kalli yadda suke cin abinci tare da Babansu be burge ka ba Yaya?”

Ya daga kai ya kalli gurin kamin ya dube yana sauke ajiyar zuciya.

“Wata rana ina jin kamar hakan zai faru amman na san ba zai taba faruwa ba”

“Kin cika tunani da yawa, a kawo miki wani abu zaki ci?”

Na saka hannuna da kaina na share hawayen da suka sake zubo min na dubi Yaya dake sanye da uniform din gurin sai tausayinsa ya kama ni, na san yayana ba mutum ne mai son zaman banza ba, yana da kokarin nema, saboda dukanmu mun taso a rayuwar talauci mun san babu kuma mun saba da hakan. A aljihunsa ake samun kudin chefane gidanmu a kullum kuma da kudinshi Mama take zuba adashe tana mana tanadin kayan aure.

“Wa zai biya? Ni ba ruwana bana da ko shishi...”

Yayi dariya domin ya san kadan daga halina ne zan iya komai ko bana da ko sisi sai dai duk abun da zai faru ya faru.

“Za a cire salary”

“Toh a kawo, daman Yaya ban ci komai ba tun safe, kuma ban taba cin abinci a Restaurant ba”

“Me kika so?”

“Akawo naman kaza da na kayan ciki da shawarma da pizza da...”

Ban gama zanawa ba ya katsene.

“Ke fa baki da hankali, duk plate daya a nan 5k plate nawa zaki ci?”

Na bude baki na kalli mutanen gabana na kirga si na kirga kudin da za su kashe.

“Tab toh Yaya a kawo kaza”

“Kaza 10k ne ke kuma abun da zaki ci ba zai wuce 2k”

“Toh ai ka ce 5k ne plate”

TA ƘI ZAMAN AURE...Onde as histórias ganham vida. Descobre agora