A SANADIN SOYAYYAR MINTI

731 17 3
                                    

*∆ A SANADIN SOYAYYAR MINTI ∆*
    _na ɓata rayuwata😭_

      Na
*Jameey yar'mutan kankia ce❣️*

*MANAZARTA WRITERS ASSOC📚🖊️*
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
_________________

*Gajeran labari*
*Labarin gaskiya (true life story)*

https://chat.whatsapp.com/BS0N4RFqbe6LFqlXZZ9vxD

*my real fan's kusan dai cewa na tafi hutu, ba zaku sake jina ba sai wani lokaci wanda nida ku bansan lokacin ba har sai Allah ya nuna mana zamu sanshi, sai gashi wata baiwar Allah tayi man magana akan nayi hakuri na rubuta labarinta dan masu irin halinta sunji su daina, idan ma akawai masu niyar farawa suma su daina idan sukaji abunda ya faru a kanta bisa da biye ma zuciya da tayi har ta aikata SOYAYYAR MINTI WATO A TURANCE ROMANTIC LOVE, da naso nace ba zani ansa ba, yanda ta nuna man damuwa da kuma nuna man amfanin labarin da taimakon da zaiyi shiyasa na ansa nace zanyi amman zanyi shi a GAJERAN LABARI duk da ita ba a short ta bani shi ba, ta bani shi a long story nice nayi summarize din shi na maida shi short saboda karda munayi mu koma school na ajiye shi ba tare da mun gama ba wannan kenan*

*Abunda nike so daku shine kuyi comment sosai hakan zai bani kwarin giwwar baku shi cikin sati insha Allah*

_Godiya ta musamman zuwa ga_
*Zauren Yar'mutan kankia fan's group*
*Real jameey novel fans 1&2*
*Sansanin Yar'mutan kankia*
*Zee-abu hausa novel*
*Ban raina allura ba fan's*
*zauren manazarta fans*
_Da dai sauransu duk ina maka godiya ta gareku_

*oyoyoyo! Ina maki murnar dawowa duniyar yanar gizo social media kenan, kawata aminiyata wato FJ marubuciyar BAGIJJA, Allah yasa kin dawo sa'a kuma a cigaba da suburbudo mana zafafan novel mana shan karatu❣️*

*Wanann page din naki ne Real eeshow marubuciyar BAN RAINA ALLURA BA!  ITAMA KARFE CE kiyi yanda kike so dashi🤗*

Page 1⏩2

Wata macece wanda bata wuce shekara 50 ba zaune a madaidacin parlourn gidansu ba abunda taje sai aikin kuka dan abun duniya ya taro yayi mata yawa, wata yarinya ce ta fito daga cikin wani daki ta zauna kasa kusa da kafar  matar itama kukan take, dan ta rasa mai zata ce ma mahaifiyar tata kallonta tayi sanann tace.

"Mama Dan Allah kiyi hakuri ki yafeman wallahi ba zan sake ba, nayi maki wannan alkwarin, wallahi sherin she... Tas! Mama ta wanke ta mari tana nuna ta da yatsa cikin fushi ta fara cewa. "Allah ya tsine maki albarki insha Allah ba zaki gama da duniya lahira ba Khadija, tunda har kika sa na zubda hawaye saboda dake kika jaman zagi a cikin unguwa, Allah ya i...  Da sauri Khadija ta rike kafafun Maman tata, tana girgiza mata kai tana hawaye masu ciwo dan kukan ma ya gagareta dan tana cikin tashin hankali ba kadan ba, yanda Maman tata take tsine mata tana mata fatan masifa ta fada mata bayan kuma itace uwa gareta mahaifiya, cikin tashin hankali tace. "Mama dan Allah ki barni haka karda abun yayi man yawa kin tsine man sannan kuma zakiyi man Allah ya isa, nasan ko baki ce man Allah ya isa ba ni tawa rayuwar tazo karshe tunda har ta dalilina kika zubda hawaye, Dan Allah Mama ki yafeman wallahi ba zan sake ba, kiyiman Uzuri Ma... Katse ta Mama ta sake yi ta hana Khadija magana, wurga mata hararar tsana tayi sannan tace. "Wallahi Khadija na tsaneki bani sonki a yanzun bani kaunar ganinki, ke har wani uzuri zan maki Khadija? Bayan cikin shegene a jikinkinki duk tarbiyar da ba baki, abu daya nike so ki sani bani bake har abada, karki sake kirana da sunan Mama ta na yafeki daga cikin ƴa'ƴana, ki kirani da suna HAFSAT dan yanzun ni ba mahaifiyar ki bace, Allah ya tseni maki albarka."

Allah Sarki kuka na sake rushewa dashi dan duniya tayi man kunci bansan ya zanyi da rayuwa ta ba, sannan kuma na tsorata da yanayin da mahaifiya ta take ciki, tashi nayi na koma dakina na cigaba da kukana, wanda tunda jiya mukaje asibiti likita ya sheda mana ina dauki da karamin ciki dan wata wata nake aikin kuka, ba kukan komai nike ba Ila kukan dana sani da biye ma son zuciyata, yunwa naji ta taso man Kuma bani sha'awar cin komai sai dan'wanke da manja da yaji wanda yaji tabarnuwa da kayan kamshi na yaji, tashi nayi na fito parlour tadda Mama nayi zaune tana share hawaye matsawa nayi kusa da ita nace. "Mama yunwa nike ji Kuma dan'wake nike son nace." Ji nayi Mama ta wanke ni da mari cikin zafin rai tace. "Wallahi baki da kwanon abinci a gidan nan, kije wanda wanda yayi maki cikin ki gaya mashi abunda kike son ci, sannan Kuma karki sake kirana da sunan mama  na gaya maki tsinanniya lalataiciya dake."

Kasa motsi nayi, ba abunda nike sai hawaye dan ni yanzun na kasa kuka ma, ji nike daman nike kukan da Mama take da naji saukin abunda nike ji a raina, hakuri na sake bata sannan na tashi na koma dakina inajin yanda yunwa take azabzabata na rasa yanda zanyi gashi bani son cin  komai idan ba dan'wake ba, haka na wuni a daki a ranar banda sake fitowa waje ba, balle har Mama ta ganni ta sake tsineman, tun karfe 1 nike zaune inajin yunwa har karfe hudun marece yayi, tunowa nayi inada wasu kudi da Nura ya bani tunin dadewa, cikin sauri na tashi na dauko kudin na zura hijab dina dan zuwa nema ma ciki abunda zan sama shi, ina fitowa na tadda Mama da Yaya Aisha sun hada kai suna kuka, Yaya Aisha Yayata ce wanda muke uwa daya uba daya, da yake nice Auta a gidanmu yanda na gansu ne hankali ya tashi dan nasan kukan da suke tsaye nayi ina kallonsu nima a zubda hawaye, kallona sukayi lokaci guda suna man wani irin kallo wannan kallo ba komai bane illa kallon tsana dan Ina ganin tsantsan tsana a cikin kwayar idonsu, ta sowa Yaya Aisha tayi ta nufoni  gadan gadan ni Kuma ina ja da baya haka muka kamayi har muka kai karshen bango, kulle idona nayi dan nasan ba dadi zatayi man ba, kamani tayi ta fara wanka man mari tana zagina, nan suka rufeni da bugu ita da Mama, tun ina yi basu hakuri har nazo da na kasa sai dai ido, tun ina gane idan nike har ta kai da bani gane mai akeyi, haka suka kama buguna suka barni kwance sheɗashaɗa cikin jini rai hannu ga Allah, ba su damu da wani hali nike ciki ba, tun la'asar sukayi man haka suka yashar dani suka cigaba da hidimar gabansu, Yayane ya shigo Jamilu shine yana da matarshi kuma shine babba a gidanmu, yana shigowa ya taddani cikin wanann halin kallon Mama yayi sannan yace.

"Mama mai yasamu Auta na ganta kwance cikin jini kuma hankalinku kwance harda ke Aisha."?

Cikin fushi yayi tambayar dan yasan abunda ke faruwa dani likitin da yaga mana ina da ciki shi ya kirashi waya ya gaya mashi halin da ake ciki da yake abokinshi ne, kallon shi Mama tayi sannan tace. "Jamilu Khadija cikin shege tayi gaya maka ne banyi ba, dan na fiddata daga cikin jerin ƴa'ƴana, baku ba Khadija kuma kabarta ta mutu, idan taso nima akashe ba damuwa ta bane."

Kallonta yayi ya fara cewa. "Haba Mama ya kamata ki yarda da kaddara mai kyau da marar kyau shine cikon imani, kisani wannan cikin yana cikin zanar kaddarar Auta dole sai tayi wannan cikin wallahi kaddararta ne, banyi tunanin ganin haka daga gareki ba Mama, kuma ke Ai... Wanke shi Mama tayi da mari tana cewa. "Har ni zaka gaya man kaddara Jamilu, inace nice na haifeka va kaine ka haifi kanka ba, tun kafin ka zama mutun nasan zanar kaddara, balle kace man wata kaddara wallahi Jamilu badan nakai zuciya nesa ba kaima da na tsine maka wallahi mutun banza, ka fita ido na kulle daman ace da ka haifi namiji kwara mace dan ita mace itace tasan kishin uwarta daman ace ciwon ƴ'a mace na ƴ'a mace ne."

Tunda Mama ta mari Yaya Jamilu bai sake cewa komai ba, sai ma zuwa da yayi zai dauke ni ya kaine asibiti domin cito da rayuwata cikin fushi Mama tace. "Mudun ka dauketa sai na tsine maka albarka Jamilu."

Share
Comment
And
Vote

A SANADIN SOYAYYAR MINTI Where stories live. Discover now