Free page (Chapter 13)

70 8 0
                                    

@fatymasardauna

*PART OF OUR DESTINY*

*(This book is mainly for those that pay, if you know you didn't pay please don't read it, here's the account number for people that are willing to pay-2268498748 Fatima Abubakar Uba bank, amount 500, WhatsApp number 07069917168)*

(Don't forgot to follow me on ArewaBooks @fatymasardauna)

*Free page*
*Chapter 13*

Dogon numfashi yaja, tare da sauk'e k'akk'arfar ajiyar zuciya, ahankali cikin rashin kuzarin daya samu kansa aciki, ya sake bud'e idanunsa, da niyar sake zura mata su, amma akasin hakan a wannan karon ido cikin ido sukayi, domin dama ba bacci take yi ba, wanda jin alamun mutum ya shigo ne yasa ta bud'e idanun nata.
Sassanyan numfashi ya fesar, tare da d'an k'alalo Murmushi ya d'aura akan kyakkyawar fuskar sa, ahankali ya nufo inda take kwancen, kana cikin sanyin murya yace.

"Ashe ba bacci kike yi ba, likimo kikayi kamar me bacci, so ya jikin naki?"

Shiru tayi tana me tsura masa idanunta, batare da tace komai ba, wanda hakan yasa shi juyowa shima ya kalleta, da idanunsa wanda suka tilasta mata janye nata idanun, lokaci d'aya saiga hawaye sun biyo kan k'uncinta.
Idanunsa ya d'an tsura mata na wasu y'an seconds, abayyane yake iya hango damuwar dake zuciyarta, wanda hakan yasa shi, d'an sunkuyowa, ahankali ya zauna akusa da k'afafunta, tare da jingina bayansa da wata y'ar k'aramar kujerar dake gaban Console, wanda akan console dinne Amma ta ajiye mata plate din, chicken penne Alfredo, da kuma wani karamin bowl wanda yake d'auke da Dynamite shrimp aciki, kallon plate din yayi, ahankali yana me kuma sake kallonta, dan baiga alaman taci abincin ba ko kad'an.

Hakan yasa shi gyara zama, atausashe yace.
"Har yanzu kina jin ciwo ajikin ki ne?"
Yayi mata tambayar yana me tsare ta da idanunsa, da suka sata sake duk'unk'une jikinta, ahankali ta d'aga masa kanta alaman "Eh."
Duk da kuwa bawai ciwon sosai take ji ba, saboda sanyata acikin ruwan d'umi da Amma keyi yana matukar rage mata pain din da take ji.

"Okay tell me inane ke miki ciwo? nunamin sai na miki allura awajen ko zai daina ciwo."
Yayi maganan yana me juyowa sukayi facing juna.
Wanda hakan yasa da sauri ta zabura ta tashi, cike da tsoro ta fara girgiza masa kai, kana murya araunace cikin yanayin yarinta had'i da tsantsar shagwab'an daya zame mata jiki tace.

"Nifa banason allura, dan Allah Karka min."

"Da gaske?"
Ya tambaya.
"Eh."
Ta amsa tana me karyar da wuyanta gefe.

"Okay indai da gaske ne bakya son allura to kici abinci, idan ba haka ba kuma allura ya zama dole."
Ya fad'a yana me jawo plate da bowl din abincin ya ajiye agabanta.
"Eat."
Kai ta girgiza, yayinda sabin hawayen da suka cika idanunta suka soma gangarowa, sunan
"Khalty."
Ta fad'a ahankali tana me yin raurau da idanunta.

Wanda hakan yasa shi fesar da numfashi, anutse yace.
"Yau bata zo bane?"

Kai ta jinjina masa alaman "Eh"

"Okay don't worry zata zo gobe in sha Allah, Amma sai in kina cin abinci, idan baki cin abinci ba zata zo ba."
Yayi maganan yana me sake matso da plate din abincin gabanta.
"Maza ci."
Ya fad'a cikin kulawa, tare da komawa Dr.Emraan dinsa na asali.
Bisa dole ahankali bawai dan tana so ba, ta jefa hannunta acikin abincin, nasu wanda ita sam bawai ta saba cin irinsu bane, duk kallon wani iri takewa abincin, amma takan rasa dalilin tsoron yi masa musu, atunaninta ko tsananin tsoron alluran da take yi ne ya jawo mata hakan, abincin ta soma ci ahankali da hannayenta wanda ke rawa, saidai kamar ko yaushe bata wani ci sosai ba ta zare hannunta, idanunsa ya d'ago ya kalleta, da sauri ta girgiza masa kai alaman ta koshi.

PART OF OUR DESTINY Where stories live. Discover now