RASHIN HAIHUWA
GORGEOUS WRITERS FORUM
G.WFHome of gorgeous, intelligent and experts writers,we are the best among the rest
Kuyi hakuri da jina shiru wuyana ke ciwo sosai,amma insha Allahu dana ji sauki update sai kun gaji da ganinsu
Page 19
Ahlam na hango ta sakale hannunta jikin na hameed, suna taka matakallan jirgi a hankali,
Rahma tana bayansu kamar wata yar rakiya
Sai kumbure kumbure take, tsaki tayi cikin ranta tareda cewa "dalla ni malamai idan zakuyi tafiya kuyi, ko kuma ku ba masu Wucewa wuri" amma kamar da gini take magana
Bakinciki kamar ya kasheta
Zuwa tayi ta bangajesu ta shige,
Nan ma ko kulata basuyiba haka taje
tazauna a kujerar dake karshe don ita a Nata tunanin ai dole a tsakiya zai zauna , nan tafara shirya abubuwa iri iri aranta
can tayi murmushi tace"uhum tun anan zanfara kunsamiki takaici(Niko nace kodai a kunsa miki ba )
Su kowa koda suka shigo suka ganta kekam a zaune sai harare harare take,
Ahlam ce tafara shigewa ta zauna a bakin window shi kuma ya zauna a tsakiya
Kwantar da kanta tayi a kafadansa shiko yana shafa mata kai
Sanarwa akayi akan jirgi zai tashi
nan fa gwalgwal aka Fara zare idon munahinci wai ita a dole tsoro take ji, tana jin jirgi yafara tashi tabi ta ririke shi ta shishige jikinshi tana cewa "wayyo my man nifa tsoro nakeji, wayyo zamu fadi, kaji kuwa yanda yakeyi ....."
Nan tafara kukan shagwaba shiko sukuku yayi yana kallonta ,
Ahlam kuwa dama harta Dan fara bacci taji an bigeta bude ido tayi,
Mizata gani Rahma a jikin hameed dinta lallai ma namiji kamar ba dazu yagama yimata dadin baki ba akan shifa ko ganinta bayi son yi .
amma yanzu gata jikinsa
wata zuciyarce ta kwabeta ai koma miye matarsa ce istigfari tayi sanna ta kauda kanta zuwa window tafara kallon sararin samaniya
Hameed kuwa sai kokarin kwace kansa yake amma ina tarirrikeshi kam masifa yafara mata "ke dallah Malama ki cikani " amma ko gizau bata yiba,
ta cusa kanta cikin rigarshi tana ta masa kukan shagwaba, shiko bakin ciki kamar ya kasheshi tsoronsa kar Ahlam tajiyo tagansu a haka
aikuwa kamar dawasa yajiyo tajiyo caraf suka hada ido murmushi tamasa sannann tajuya shiko kunya kamar kasa ta bude ya shige ciki
Mutuniyar kuwa tana nan takara lafewa,
Jin yayi shiru ya daina kwatar kansa yasata tunanin yasaduda
nan kowa bata San cewa bari yayi saita sake sannan yayi maganinta
Can harsunyi nisa yaji tafara sauke numfashi alamar tayi bacci, saida ya hada duk karfinshi sannna ya tunkudata saigata tana lilo ita bata fadi kasa ba sbod sit bealts din dake jikinta,
tana cikin mafarki waigata nan ita da hameed dinta sunata shawagi a sararin samaniya, sai kuma taji kamar dagaske ma yawon take,
ai a tsoro ce ta tashi , sai ganinta tayi tana lilo tsakanin kujera (hhhhhh)
dakyar tasamu takoma tazauna
kana takalli hameed taga yajuya wurin Rabin ransa sunata hira harda dariya da tafawa
Tab amma man din nan yama raina Mata sense wato shiya hankadota
Amma a hankali zaidawo hannuntaA wurin fitowa ma anyi didima domin suna fitowa tayi saurin makale hannunta a nasa wai duk dan taba Ahlam haushi
Itakuwa baiwar Allah murmushi kawai tayi tawucesu taje ta shiga motar datazo daukarsu
Shiko dasauri ya cire hannunta a jikinsa tare da nuna ta da Dan yatsa game dacewa '
"Ke wallahi bari namiki last warning idan kika kara tabani wlh saina babballaki banza mahaukaciya ke idan kinsan yadda na natsaneki da baki kwatanta rabata wlh "
"Abdul nikuma ina sonka so marar musalatuwa kaima da kasan irin sondanake maka da bazakace ka tsanine ba haba Abdul miye ajikin wancar banzar da babu a jikina "
Tsaki yayi ya wuce domin a ganinshi magana da ita bata lokaci ne .......
•••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••
Find me on wattpad at FateemaAdamu
Fatima Adamu Gamawa AKA Fateegamawah
Insha Allahu anjima ma zakujini
Finishing😝
![](https://img.wattpad.com/cover/181898347-288-k23306.jpg)
YOU ARE READING
RASHIN HAIHUWA
Non-FictionAhlam baiwar Allah ce wanda bata taba haihuwa ba har tayi shekara goma da aure gashi yan uwan miji sun takura mata har sukasa yayi aure cikin ikon Allah kuwa ita matar daya auran ta haihu sai take tama gori da rashin mutumci